< Fitowa 14 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Forsothe the Lord spak to Moises, and seide, Speke thou to the sones of Israel;
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
turne thei ayen, and sette thei tentis euene ayens Fiayroth, which is bitwixe Magdalum and the see, ayens Beelsefon; in the siyt therof ye schulen sette tentis ouer the see.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
And Farao schal seie on the sones of Israel, Thei ben maad streit in the lond, the deseert hath closid hem to gidere.
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
And Y schal make hard his herte, and he schal pursue you, and Y schal be glorified in Farao, and in al his oost; and Egipcians schulen wite that Y am the Lord; and thei diden so.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
And it was teld to the kyng of Egipcians, that the puple hadde fled; and the herte of Farao and of hise seruauntis was chaungid on the puple, and thei seiden, What wolden we do, that we leften Israel, that it schulde not serue us?
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
Therfor Farao ioynede the chare, and took with him al his puple;
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
and he took sixe hundrid chosyn charis, and what euer thing of charis was in Egipt, and duykis of al the oost.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
And the Lord made hard `the herte of Farao, kyng of Egipt, and he pursuede the sones of Israel; and thei weren go out in an hiy hond.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
And whanne Egipcians pursueden the steppis of the sones of Israel bifor goynge, thei founden hem in tentis on the see; al the chyualrye and charis of Farao, and al the oost weren in Fiayroth, ayens Beelsefon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
And whanne Farao hadde neiyed the sones of Israel, reisiden her iyen, and thei sien Egipcians bihynde hem, and dredden greetli; and thei crieden to the Lord,
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
and seiden to Moises, In hap sepulcris weren not in Egipt, therfor thou hast take vs awei, that we schulen die in wildirnesse? what woldist thou do this, that thou leddist vs out of Egipt?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
Whether this is not the word which we spaken to thee in Egipt, `and seiden, Go awei fro vs, that we serue Egipcians? for it is myche betere to serue hem, than to die in wildirnesse.
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
And Moises seide to the puple, Nyle ye drede, stonde ye, and `se ye the grete werkys of God, whiche he schal do to dai; for ye schulen no more se Egipcians, whiche ye seen now, til in to with outen ende;
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
the Lord schal fiyte for you, and ye schulen be stille.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
And the Lord seide to Moises, What criest thou to me? Speke thou to the sones of Israel, that thei go forth; forsothe reise thou thi yerde,
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
and stretche forth thin hond on the see, and departe thou it, that the sones of Israel go in the myddis of the see, by drie place.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
Forsothe Y schal make hard the herte of Egipcians, that thei pursue you, and Y schal be glorified in Farao, and in al the oost of hym, and in the charis, and in the knyytis of hym;
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
and Egipcians schulen wite that Y am the Lord God, whanne Y schal be glorified in Farao, and in the charis, and in the knyytis of hym.
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
And the aungel of the Lord, that yede bifore the castellis of Israel, took hym silf, and yede bihynde hem; and the piler of cloude yede to gidir with hym, and lefte the formere thingis aftir the bak,
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
and stood bitwixe the `castels of Egipcians and castels of Israel; and the cloude was derk toward Egipcians, and liytnynge `the nyyt toward `the children of Israel, so that in al the tyme of the niyt thei miyten not neiy togidere to hem silf.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
And whanne Moises hadde stretchid forth the hond on the see, the Lord took it awei, the while a greet wynde and brennynge blew in al the niyt, and turnede in to dryenesse; and the watir was departid.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
And the sones of Israel entriden by the myddis of the drye see; for the watir was as a wal at the riyt side and left side of hem.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
And Egipcians pursueden, and entriden aftir hem, al the ridyng of Farao, hise charis, and knyytis, bi the myddis of the see.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
And the wakyng of the morewtid cam thanne, and lo! the Lord bihelde on the castels of Egipcians, bi a piler of fier, and of cloude, and killide the oost of hem; and he destriede the wheelis of charis,
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
and tho weren borun in to the depthe. Therfor Egipcians seiden, Fle we Israel; for the Lord fiytith for hem ayenus vs.
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
And the Lord seide to Moises, Holde forth thin hond on the see, that the watris turne ayen to Egipcians, on the charis, and knyytis of hem.
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
And whanne Moises hadde hold forth the hoond ayens the see, it turnede ayen first in the morewtid to the formere place; and whanne Egipcians fledden, the watris camen ayen, and the Lord wlappide hem in the myddis of the floodis.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
And the watris turneden ayen, and hiliden the charis, and knyytis of al the oost of Farao, which sueden, and entriden in to the see; sotheli not oon of hem was alyue.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
Forsothe the sones of Israel yeden thorouy the myddis of the drye see, and the watris weren to hem as for a wal, on the riyt side and left side.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
And in that dai the Lord delyuerede Israel fro the hond of Egipcians, and thei sien Egipcians deed on the brynke of the see,
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
and thei seiyen the greet hond which the Lord hadde vsid ayens hem; and the puple dredde the Lord, and thei bileueden to the Lord, and to Moises his seruaunt.