< Fitowa 14 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Then Yahweh spoke to Moses, saying,
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
“Say to the Israelites that they should turn and camp before Pi Hahiroth, between Migdol and the sea, before Baal Zephon. You are to camp by the sea opposite Pi Hahiroth.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
Pharaoh will say about the Israelites, 'They are wandering in the land. The wilderness has closed in on them.'
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
I will harden Pharaoh's heart, and he will pursue them. I will get honor because of Pharaoh and all his army. The Egyptians will know that I am Yahweh.” So the Israelites camped as they were instructed.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
When the king of Egypt was told that the Israelites had fled, the minds of Pharaoh and his servants turned against the people. They said, “What have we done? We have released Israel from serving us.”
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
Then Pharaoh got his chariots ready and took his army with him.
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
He took six hundred chosen chariots and all the other chariots of Egypt, with officers on all of them.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
Yahweh hardened the heart of Pharaoh, king of Egypt, and the king pursued the Israelites. Now the Israelites had gone away in triumph.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
But the Egyptians pursued them, together with all his horses and chariots, his horsemen, and his army. They overtook the Israelites camping by the sea beside Pi Hahiroth, before Baal Zephon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
When Pharaoh came close, the Israelites looked up and were surprised. The Egyptians were marching after them, and they were terrified. The Israelites cried out to Yahweh.
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
They said to Moses, “Is it because there were no graves in Egypt, that you have taken us away to die in the wilderness? Why have you treated us like this, bringing us out of Egypt?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
Is this not what we told you in Egypt? We said to you, 'Leave us alone, so we can work for the Egyptians.' It would have been better for us to work for them than to die in the wilderness.”
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
Moses said to the people, “Do not be afraid. Stand still and see the rescue that Yahweh will provide for you today. For you will never see again the Egyptians whom you see today.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
Yahweh will fight for you, and you will only have to stand still.”
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
Then Yahweh said to Moses, “Why are you, Moses, continuing to call out to me? Tell the Israelites to go forward.
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
Lift up your staff, reach out with your hand over the sea and divide it in two, so that the people of Israel may go through the sea on dry ground.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
Be aware that I will harden the Egyptians' hearts so they will go after them. I will get honor because of Pharaoh and all his army, his chariots, and his horsemen.
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
Then the Egyptians will know that I am Yahweh when I have gotten honor because of Pharaoh, his chariots, and his horsemen.”
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
The angel of God, who went before the Israelites, moved and went behind them. The pillar of cloud moved from before them and went to stand behind them.
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
The cloud came between the camp of Egypt and the camp of Israel. It was a dark cloud to the Egyptians, but it lit the night for the Israelites, so one side did not come near the other all night.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
Moses reached out with his hand over the sea. Yahweh drove the sea back by a strong east wind all that night and made the sea into dry land. In this way the waters were divided.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
The Israelites went into the middle of the sea on dry ground. The waters formed a wall for them on their right hand and on their left.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
The Egyptians pursued them. They went after them into the middle of the sea—all Pharaoh's horses, chariots, and horsemen.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
But in the early morning hours, Yahweh looked down on the Egyptian army through the pillar of fire and cloud. He caused panic among the Egyptians.
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
Their chariot wheels were clogged, and the horsemen drove with difficulty. So the Egyptians said, “Let us flee from Israel, for Yahweh is fighting for them against us.”
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
Yahweh said to Moses, “Reach out with your hand over the sea so that the waters may come back onto the Egyptians, their chariots, and their horsemen.”
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
So Moses reached out with his hand over the sea, and it returned to its normal course when the morning appeared. The Egyptians fled into the sea, and Yahweh drove the Egyptians into the middle of it.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
The waters came back and covered Pharaoh's chariots, horsemen, and his entire army that had followed the chariots into the sea. No one survived.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
However, the Israelites walked on dry land in the middle of the sea. The waters were a wall for them on their right hand and on their left.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
So Yahweh saved Israel that day out of the hand of the Egyptians, and Israel saw dead Egyptians on the seashore.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
When Israel saw the great power that Yahweh used against the Egyptians, the people honored Yahweh, and they trusted in Yahweh and in his servant Moses.

< Fitowa 14 >