< Fitowa 14 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Then the Lord spake vnto Moses, saying,
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Speake to the children of Israel, that they returne and campe before Pi-hahiroth, betweene Migdol and the Sea, ouer against Baal-zephon: about it shall ye campe by the Sea.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
For Pharaoh will say of the children of Israel, They are tangled in the land: the wildernesse hath shut them in.
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
And I will harden Pharaohs heart that hee shall follow after you: so I will get mee honour vpon Pharaoh, and vpon all his hoste: the Egyptians also shall knowe that I am the Lord: and they did so.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
Then it was told the King of Egypt, that the people fled: and the heart of Pharaoh and of his seruants was turned against the people, and they sayde, Why haue we this done, and haue let Israel go out of our seruice?
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
And he made ready his charets, and tooke his people with him,
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
And tooke sixe hundreth chosen charets, and all the charets of Egypt, and captaines ouer euery one of them.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
(For the Lord had hardened the heart of Pharaoh king of Egypt, and he followed after the children of Israel: but the children of Israel went out with an hie hand)
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
And the Egyptians pursued after them, and all the horses and charets of Pharaoh, and his horsemen and his hoste ouertooke them camping by the Sea, beside Pi-hahiroth, before Baal-zephon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
And when Pharaoh drew nie, the children of Israel lift vp their eyes, and beholde, the Egyptians marched after them, and they were sore afrayde: wherefore the children of Israel cried vnto the Lord.
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
And they sayde vnto Moses, Hast thou brought vs to die in the wildernes, because there were no graues in Egypt? wherefore hast thou serued vs thus, to carie vs out of Egypt?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
Did not wee tell thee this thing in Egypt, saying, Let vs be in rest, that we may serue the Egyptians? for it had bene better for vs to serue the Egyptians, then that wee shoulde dye in the wildernesse.
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
Then Moses sayde to the people, Feare ye not, stand still, and beholde the saluation of the Lord which he will shew to you this day. For the Egyptians, whome ye haue seene this day, ye shall neuer see them againe.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
The Lord shall fight for you: therefore hold you your peace.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
And the Lord sayd vnto Moses, Wherefore cryest thou vnto me? speake vnto the children of Israel that they go forward:
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
And lift thou vp thy rod, and stretche out thine hand vpon the Sea and deuide it, and let the children of Israel goe on drie ground thorow the middes of the Sea.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
And I, beholde, I will harden the heart of the Egyptians, that they may follow them, and I wil get me honour vpon Pharaoh, and vpon all his host, vpon his charets, and vpon his horsemen.
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
Then the Egyptians shall know that I am the Lord, when I haue gotten me honour vpon Pharaoh, vpon his charets, and vpon his horsemen.
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
(And the Angel of God, which went before the hoste of Israel, remoued and went behinde them: also the pillar of the cloude went from before them, and stoode behinde them,
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
And came betweene the campe of the Egyptians and the campe of Israel: it was both a cloude and darkenes, yet gaue it light by night, so that all the night long the one came not at the other)
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
And Moses stretched forth his hande vpon the Sea, and the Lord caused the sea to runne backe by a strong East winde all the night, and made the Sea dry land: for the waters were deuided.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
Then the children of Israel went through the middes of the Sea vpon the drie ground, and the waters were a wall vnto them on their right hand, and on their left hand.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
And the Egyptians pursued and went after them to the middes of the Sea, euen all Pharaohs horses, his charets, and his horsemen.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
Nowe in the morning watche, when the Lord looked vnto the hoste of the Egyptians, out of the firie and cloudie pillar, he strooke the host of the Egyptians with feare.
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
For he tooke off their charet wheeles, and they draue them with much a doe: so that the Egyptians euery one sayd, I wil flee from the face of Israel: for the Lord fighteth for them against the Egyptians.
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
Then the Lord sayde to Moses, Stretche thine hand vpon the Sea, that the waters may returne vpon the Egyptians, vpon their charets and vpon their horsemen.
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
Then Moses stretched forth his hand vpon the Sea, and the Sea returned to his force early in the morning, and the Egyptians fled against it: but the Lord ouerthrew the Egyptians in the mids of the Sea.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
So the water returned and couered the charets and the horsemen, euen all the hoste of Pharaoh that came into the sea after them: there remained not one of them.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
But the children of Israel walked vpon dry land thorowe the middes of the Sea, and the waters were a wall vnto them on their right hande, and on their left.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
Thus the Lord saued Israel the same day out of the hand of the Egyptians, and Israel sawe the Egyptians dead vpon the Sea banke.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
And Israel saw the mightie power, which the Lord shewed vpon the Egyptians: so the people feared the Lord, and beleeued the Lord, and his seruant Moses.

< Fitowa 14 >