< Fitowa 14 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord said to Moses,
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Give orders to the children of Israel to go back and put up their tents before Pi-hahiroth, between Migdol and the sea, in front of Baal-zephon, opposite to which you are to put up your tents by the sea.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
And Pharaoh will say of the children of Israel, They are wandering without direction, they are shut in by the waste land.
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
And I will make Pharaoh's heart hard, and he will come after them and I will be honoured over Pharaoh and all his army, so that the Egyptians may see that I am the Lord. And they did so.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
And word came to Pharaoh of the flight of the people: and the feeling of Pharaoh and of his servants about the people was changed, and they said, Why have we let Israel go, so that they will do no more work for us?
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
So he had his war-carriage made ready and took his people with him:
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
And he took six hundred carriages, all the carriages of Egypt, and captains over all of them.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
And the Lord made the heart of Pharaoh hard, and he went after the children of Israel: for the children of Israel had gone out without fear.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
But the Egyptians went after them, all the horses and carriages of Pharaoh, and his horsemen, and his army, and overtook them in their tents by the sea, by Pihahiroth, before Baal-zephon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
And when Pharaoh came near, the children of Israel, lifting up their eyes, saw the Egyptians coming after them, and were full of fear; and their cry went up to God.
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
And they said to Moses, Was there no resting-place for the dead in Egypt, that you have taken us away to come to our death in the waste land? why have you taken us out of Egypt?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
Did we not say to you in Egypt, Let us be as we are, working for the Egyptians? for it is better to be the servants of the Egyptians than to come to our death in the waste land.
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
But Moses said, Keep where you are and have no fear; now you will see the salvation of the Lord which he will give you today; for the Egyptians whom you see today you will never see again.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
The Lord will make war for you, you have only to keep quiet.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
And the Lord said to Moses, Why are you crying out to me? give the children of Israel the order to go forward.
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
And let your rod be lifted up and your hand stretched out over the sea, and it will be parted in two; and the children of Israel will go through on dry land.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
And I will make the heart of the Egyptians hard, and they will go in after them: and I will be honoured over Pharaoh and over his army, his war-carriages, and his horsemen.
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
And the Egyptians will see that I am the Lord, when I get honour over Pharaoh and his war-carriages and his horsemen.
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
Then the angel of God, who had been before the tents of Israel, took his place at their back; and the pillar of cloud, moving from before them, came to rest at their back:
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
And it came between the army of Egypt and the army of Israel; and there was a dark cloud between them, and they went on through the night; but the one army came no nearer to the other all the night.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
And when Moses' hand was stretched out over the sea, the Lord with a strong east wind made the sea go back all night, and the waters were parted in two and the sea became dry land.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
And the children of Israel went through the sea on dry land: and the waters were a wall on their right side and on their left.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
Then the Egyptians went after them into the middle of the sea, all Pharaoh's horses and his war-carriages and his horsemen.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
And in the morning watch, the Lord, looking out on the armies of the Egyptians from the pillar of fire and cloud, sent trouble on the army of the Egyptians;
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
And made the wheels of their war-carriages stiff, so that they had hard work driving them: so the Egyptians said, Let us go in flight from before the face of Israel, for the Lord is fighting for them against the Egyptians.
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
And the Lord said to Moses, Let your hand be stretched out over the sea, and the waters will come back again on the Egyptians, and on their war-carriages and on their horsemen.
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
And when Moses' hand was stretched out over the sea, at dawn the sea came flowing back, meeting the Egyptians in their flight, and the Lord sent destruction on the Egyptians in the middle of the sea.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
And the waters came back, covering the war-carriages and the horsemen and all the army of Pharaoh which went after them into the middle of the sea; not one of them was to be seen.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
But the children of Israel went through the sea walking on dry land, and the waters were a wall on their right side and on their left.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
So that day the Lord gave Israel salvation from the hands of the Egyptians; and Israel saw the Egyptians dead on the sea's edge.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
And Israel saw the great work which the Lord had done against the Egyptians, and the fear of the Lord came on the people and they had faith in the Lord and in his servant Moses.

< Fitowa 14 >