< Fitowa 14 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talede til Mose og sagde:
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Tal til Israels Børn, at de drage om og lejre sig for Pi-Hakiroth, imellem Migdol og Havet, tvært over for Baal-Zefon, ret for den skulle I lejre eder ved Havet.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
Thi Farao skal sige om Israels Børn: De ere farne vild i Landet, Ørken har lukket for dem.
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
Og jeg vil forhærde Faraos Hjerte, at han skal forfølge dem, og jeg vil forherlige mig paa Farao og paa al hans Hær, og Ægypterne skulle fornemme, at jeg er Herren; og de gjorde saa.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
Og det blev Kongen af Ægypten tilkendegivet, at Folket flyede; da omvendtes Faraos og hans Tjeneres Hjerte imod Folket, og de sagde: Hvi gjorde vi dette, at vi lode Israel fare, at de ikke skulde tjene os?
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
Saa lod han spænde for sin Vogn og tog sit Folk med sig.
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
Og han tog seks Hundrede udvalgte Vogne og alle Vogne i Ægypten og Høvedsmændene over dem alle.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
Thi Herren forhærdede Ægyptens Konge Faraos Hjerte, saa at han forfulgte Israels Børn; men Israels Børn vare uddragne ved en høj Haand.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Saa forfulgte Ægypterne dem og naaede dem, da de havde lejret sig ved Havet, alle Faraos Vognheste og hans Ryttere og hans Hær, ved Pi-Hakiroth, tvært over for Baal-Zefon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
Og Farao nærmede sig; og Israels Børn opløftede deres Øjne, og se, Ægypterne droge efter dem; da frygtede de saare, og Israels Børn raabte til Herren.
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
Og de sagde til Mose: Mon der ikke var Grave i Ægypten, siden du tog os ud til at dø i Ørken? hvi gjorde du os dette, at du førte os ud af Ægypten?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
Er det ej det Ord, som vi talede til dig i Ægypten, sigende: Lad af fra os, vi ville tjene Ægypterne; thi det er os bedre at tjene Ægypterne end at dø i Ørken.
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
Da sagde Mose til Folket: Frygter ikke, bliver staaende og ser Herrens Frelse, som han skal vise eder i Dag; thi disse Ægyptere, som I se i Dag, dem skulle I ikke i al Evighed se mere herefter.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
Herren skal stride for eder, og I, I skulle tie.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
Og Herren sagde til Mose: Hvi vil du raabe til mig? sig til Israels Børn, at de skulle drage frem;
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
og opløft du din Stav og udræk din Haand over Havet og skil det ad, og Israels Børn skulle gaa midt igennem Havet paa det tørre.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
Og jeg, se, jeg vil forhærde Ægypternes Hjerte, at de skulle forfølge eder; saa vil jeg forherlige mig paa Farao og paa al hans Hær, paa hans Vogne og paa hans Ryttere.
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
Og Ægypterne skulle fornemme, at jeg er Herren, naar jeg har forherliget mig paa Farao, paa hans Vogne og paa hans Ryttere.
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
Da drog den Guds Engel, som gik foran Israels Hær, af Sted og drog bag dem; og Skystøtten drog fra deres Ansigt og stod bag dem.
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
Og den kom imellem Ægypternes Hær og imellem Israels Hær, og den var Sky og Mørke [for hine], men oplyste Natten [for disse]; og den ene kom ikke til den anden den ganske Nat.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
Og Mose udstrakte sin Haand over Havet, og Herren lod Havet fare bort ved et stærkt Østenvejr den ganske Nat og gjorde Havet som det tørre; og Vandene skiltes ad.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
Og Israels Børn gik midt igennem Havet paa det tørre; og Vandet var dem en Mur paa deres højre og paa deres venstre Side.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
Og Ægypterne forfulgte dem og droge efter dem, alle Faraos Heste, hans Vogne og hans Ryttere, til midt i Havet.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
Og det skete, der Morgenvagten kom, da saa Herren i Ildens og Skyens Støtte til Ægypternes Hær og forfærdede Ægypternes Hær.
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
Og han stødte Hjulene af deres Vogne og lod dem rykke frem med Besvær; da sagde Ægypterne: Jeg maa fly for Israel; thi Herren strider for dem imod Ægypterne.
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
Da sagde Herren til Mose: Udræk din Haand over Havet, og Vandene skulle falde tilbage over Ægypterne, over deres Vogne og over deres Ryttere.
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
Saa rakte Mose sin Haand over Havet, og Havet kom igen mod Morgenen i sit sædvanlige Leje, og Ægypterne flyede imod det; saa styrtede Herren Ægypterne midt i Havet.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
Og Vandet kom igen og skjulte i hele Faraos Hær Vogne og Ryttere, som vare komne efter dem i Havet; der blev end ikke een tilovers af dem.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
Men Israels Børn vare gangne paa det tørre midt igennem Havet, og Vandet havde været dem en Mur paa deres højre og paa deres venstre Side.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
Saa frelste Herren Israel den samme Dag af Ægypternes Haand, og Israel saa Ægypterne ligge døde ved Havets Bred.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
Og Israel saa den store Magt, som Herren havde bevist paa Ægypterne, og Folket frygtede Herren; og de troede paa Herren og paa Mose, hans Tjener.

< Fitowa 14 >