< Fitowa 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
خداوند به موسی فرمود:
2 “Keɓe mini kowane ɗan fari. Ɗan fari wanda ya fara buɗe mahaifa a cikin Isra’ilawa nawa ne, ko na mutum ko na dabba.”
«تمام نخست‌زادگان قوم اسرائیل را به من وقف کن، زیرا همۀ نخست‌زادگان، خواه انسان و خواه حیوان، به من تعلق دارند.»
3 Sai Musa ya ce wa mutane, “Ku tuna da wannan rana, ranar da kuka fito daga Masar, daga ƙasar bauta, gama Ubangiji ya fito da ku da hannu mai iko. Kada ku ci wani abin da yake da yisti.
پس موسی به قوم گفت: «این روز را که روز رهایی شما از بردگی مصر است همیشه به یاد داشته باشید، زیرا خداوند با دست توانای خود، شما را از آن رها ساخت. به خاطر بسپارید که در این روزهای عید، باید نان بدون خمیرمایه بخورید.
4 A wannan rana kuka fita, wato, a watan Abib.
امروز در ماه ابیب شما از مصر خارج می‌شوید.
5 Sa’ad da Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku, ƙasar da take zub da madara da zuma, za ku kiyaye wannan biki a wannan wata.
خداوند به اجدادتان وعده داده است که، سرزمین کنعانی‌ها، حیتی‌ها، اموری‌ها، حوی‌ها و یبوسی‌ها را به شما واگذار کند، بنابراین، وقتی شما را به سرزمینی که به”سرزمین شیر و عسل“معروف است، داخل می‌کند، باید این روز را، هر ساله جشن بگیرید.
6 Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, a kan rana ta bakwai kuma za ku yi biki ga Ubangiji.
به مدت هفت روز نان فطیر بخورید و در روز هفتم عیدی برای خداوند نگاه دارید.
7 Ku ci burodi marar yisti cikin kwana bakwai; kada a sami wani abu mai yisti a cikinku, ko a sami yisti a ko’ina a wurinku.
در این هفت روز، نان فطیر بخورید. در خانه‌های شما و حتی در سرزمین شما اثری از خمیرمایه پیدا نشود.
8 A ranan nan kowa zai faɗa wa ɗanka, ‘Ina yin haka saboda abin da Ubangiji ya yi mini, sa’ad da na fita daga Masar.’
«هر سال هنگام برگزاری این جشن، به فرزندان خود بگویید که این جشن به مناسبت آن کار بزرگی است که خداوند به خاطر شما انجام داد و شما را از مصر بیرون آورد.
9 Wannan abin tunawa zai zama muku alama a hannunku, da kuma a goshinku cewa dokar Ubangiji tana a bakinku. Gama Ubangiji ya fitar da ku daga Masar da hannu mai iko.
این جشن مانند علامتی بر دستتان یا نشانی بر پیشانی‌تان خواهد بود تا به شما یادآوری نماید که همیشه در شریعت خداوند تفکر کنید و از آن سخن بگویید، زیرا خداوند با قدرت عظیم خود، شما را از مصر بیرون آورد.
10 Dole ku kiyaye wannan farilla kowace shekara a lokacinta.
«پس هر سال در موعد مقرر این عید را جشن بگیرید.
11 “Bayan Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, ya kuma ba da ita yadda ya alkawarta muku da rantsuwa, ku da kakanninku,
«زمانی که خداوند، شما را به سرزمین کنعان که وعدهٔ آن را از پیش به اجداد شما داده بود بیاورد، به خاطر داشته باشید که
12 sai ku miƙa kowane ɗan fari ga Ubangiji. Duk ɗan farin dabbobinku na Ubangiji ne.
پسران نخست‌زادۀ شما و همچنین نخست‌زادهٔ نر حیوانات شما از آنِ خداوند می‌باشند و باید آنها را وقف خدا کنید.
13 Amma a fanshi kowane ɗan farin jakinku da ɗan rago. In kuwa ba za ku fanshe shi ba, sai ku karye wuyansa. Sai ku fanshe kowane ɗan farin daga cikin’ya’yanku.
به جای نخست‌زادهٔ الاغ، بره‌ای فدیه دهید. ولی اگر نخواستید آن را با بره عوض کنید، باید گردن الاغ را بشکنید. اما برای پسران نخست‌زادۀ خود حتماً باید فدیه بدهید.
14 “A kwanaki masu zuwa, in ɗanka ya tambaye ka, ‘Mene ne manufar wannan?’ Ka faɗa masa cewa, ‘Da hannu mai iko Ubangiji ya fito da mu daga Masar, daga ƙasar bauta.
«در آینده وقتی فرزندانتان از شما بپرسند:”این کارها برای چیست؟“بگویید:”خداوند با دست توانای خود ما را از بردگی مصری‌ها نجات بخشید.
15 Sa’ad da Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai yarda ya sallame mu ba, sai Ubangiji ya kashe dukan’ya’yan farin ƙasar Masar, na mutum da na dabba, gaba ɗaya. Domin haka nake yin hadaya ga Ubangiji da’ya’yan fari, maza, da suka fara buɗe mahaifa, amma nakan fanshi dukan’ya’yan farina maza.’
چون فرعون ما را از اسارت رها نمی‌کرد، برای همین، خداوند تمام پسران نخست‌زادۀ مصری‌ها و همچنین نخست‌زاده‌های نر حیوانات آنان را هلاک کرد تا ما را نجات دهد. به همین دلیل نخست‌زادهٔ نر حیوانات خود را برای خداوند قربانی می‌کنیم تا برای پسران نخست‌زادۀ خود فدیه دهیم.“
16 Za tă kuma zama alama a hannunku da kuma shaida a goshinku cewa Ubangiji ya fito da mu daga Masar da hannunsa mai iko.”
این جشن مانند علامتی بر دستتان و یا نشانی بر پیشانی‌تان خواهد بود تا به یاد شما آورد که خداوند با دست قوی خود ما را از مصر بیرون آورد.»
17 Sa’ad da Fir’auna ya bar mutane su tafi, Allah bai bi da su a hanyar da ta bi ta iyakar Filistiyawa ba, ko da yake wannan hanya ce ta fi kusa. Gama Allah ya ce, “In suka fuskanci yaƙi, wataƙila su canja ra’ayinsu su koma Masar.”
وقتی سرانجام فرعون به قوم اسرائیل اجازه داد تا از مصر بروند، خدا آنان را از راه اصلی که از سرزمین فلسطینی‌ها می‌گذشت نبرد، هرچند آن راه نزدیکتر بود. خدا گفت: «اگر قوم با جنگ روبرو شوند، ممکن است پشیمان شده، به مصر برگردند.»
18 Saboda haka Allah ya kewaye da mutanen ta hamada zuwa Jan Teku. Isra’ilawa kuwa suka fita daga Masar da shirin yaƙi.
پس خدا آنها را از طریق صحرایی که در حاشیهٔ دریای سرخ بود هدایت نمود. بدین ترتیب قوم اسرائیل مانند لشکری مسلح از مصر بیرون رفتند.
19 Musa ya ɗauki ƙasusuwan Yusuf tare da shi, gama Yusuf ya sa Isra’ilawa su rantse masa. Ya ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, sai ku ɗibi ƙasusuwana tare da ku daga wannan wuri.”
موسی در این سفر استخوانهای یوسف را نیز همراه خود برد، چون یوسف در زمان حیات خود بنی‌اسرائیل را قسم داده، گفته بود: «وقتی خدا شما را برهاند، استخوانهای مرا هم با خود از اینجا ببرید.»
20 Bayan sun bar Sukkot sai suka kafa sansani a Etam a bakin hamada.
پس قوم اسرائیل سوکوت را ترک کرده، در ایتام که در حاشیهٔ صحرا بود، خیمه زدند.
21 Da rana Ubangiji yakan ja gabansu a cikin al’amudin girgije domin yă bishe su a kan hanyarsu, da dare kuma a cikin al’amudin wuta domin yă ba su haske, domin su iya tafiya dare da rana.
در این سفر، خداوند ایشان را در روز به‌وسیلهٔ ستونی از ابر و در شب به‌وسیلۀ ستونی از آتش هدایت می‌کرد. از این جهت هم در روز می‌توانستند سفر کنند و هم در شب.
22 Al’amudan nan biyu, na girgije da na wuta, ba su daina yi wa jama’a jagora ba.
ستونهای ابر و آتش لحظه‌ای از برابر آنها دور نمی‌شد.

< Fitowa 13 >