< Fitowa 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et le Seigneur parla à Moïse, disant:
2 “Keɓe mini kowane ɗan fari. Ɗan fari wanda ya fara buɗe mahaifa a cikin Isra’ilawa nawa ne, ko na mutum ko na dabba.”
Consacre-moi tout premier-né, tout être qui aura ouvert des entrailles maternelles parmi les fils de mon peuple, depuis l'homme jusqu'aux bestiaux; il est à moi.
3 Sai Musa ya ce wa mutane, “Ku tuna da wannan rana, ranar da kuka fito daga Masar, daga ƙasar bauta, gama Ubangiji ya fito da ku da hannu mai iko. Kada ku ci wani abin da yake da yisti.
Moïse dit donc au peuple: Souvenez-vous de ce jour où vous êtes sortis de la terre d'Égypte et de la maison de servitude, d'où le Seigneur nous a tirés par sa main puissante: ce jour-là vous ne mangerez pas de levain
4 A wannan rana kuka fita, wato, a watan Abib.
Vous partez aujourd'hui dans la lune des nouveaux blés.
5 Sa’ad da Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku, ƙasar da take zub da madara da zuma, za ku kiyaye wannan biki a wannan wata.
Et lorsque le Seigneur vous aura conduits en la terre des Chananéens, des Hettéens, des Amorrhéens, des Évéens, des Jébuséens, des Gergéséens et des Phérézéens, terre qu'il a promis à vos pères de vous donner, terre où coulent le lait et le miel, vous observerez en cette lune cette loi religieuse.
6 Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, a kan rana ta bakwai kuma za ku yi biki ga Ubangiji.
Pendant six jours vous mangerez des azymes; le septième jour, c'est la fête du Seigneur.
7 Ku ci burodi marar yisti cikin kwana bakwai; kada a sami wani abu mai yisti a cikinku, ko a sami yisti a ko’ina a wurinku.
Vous mangerez des azymes sept jours; on ne verra pas de pain levé, vous n'aurez pas de levain en tout votre territoire.
8 A ranan nan kowa zai faɗa wa ɗanka, ‘Ina yin haka saboda abin da Ubangiji ya yi mini, sa’ad da na fita daga Masar.’
En ce jour-là, tu instruiras ton fils, disant: C'est à cause de ce qu'a fait pour moi le Seigneur lorsque nous sommes sortis d'Égypte.
9 Wannan abin tunawa zai zama muku alama a hannunku, da kuma a goshinku cewa dokar Ubangiji tana a bakinku. Gama Ubangiji ya fitar da ku daga Masar da hannu mai iko.
Et ce sera pour toi un signe, attaché à ta main, un mémorial devant tes yeux, afin que la loi du Seigneur soit sur tes lèvres; car c'est par une main puissante que le Seigneur t'a tiré de l'Égypte.
10 Dole ku kiyaye wannan farilla kowace shekara a lokacinta.
Et, dans la suite des jours, vous observerez cette loi au temps marqué.
11 “Bayan Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, ya kuma ba da ita yadda ya alkawarta muku da rantsuwa, ku da kakanninku,
Lorsque le Seigneur ton Dieu t'aura introduit en la terre des Chananéens, qu'il a promise à tes pères, et qu'il te donnera,
12 sai ku miƙa kowane ɗan fari ga Ubangiji. Duk ɗan farin dabbobinku na Ubangiji ne.
Tu mettras à part, pour le Seigneur, tout mâle ayant ouvert les entrailles de sa mère; tu consacreras au Seigneur, parmi le bétail et parmi les menus troupeaux, tout mâle qui aura ouvert les entrailles de sa mère, parmi tout ce qui naîtra, tu consacreras ainsi les mâles au Seigneur.
13 Amma a fanshi kowane ɗan farin jakinku da ɗan rago. In kuwa ba za ku fanshe shi ba, sai ku karye wuyansa. Sai ku fanshe kowane ɗan farin daga cikin’ya’yanku.
En échange de tout ânon, ayant ouvert les entrailles de l'ânesse, tu pourras donner une brebis; si tu ne l'échanges, tu en paieras la rançon; tu paieras la rançon. de tout premier-né de tes fils.
14 “A kwanaki masu zuwa, in ɗanka ya tambaye ka, ‘Mene ne manufar wannan?’ Ka faɗa masa cewa, ‘Da hannu mai iko Ubangiji ya fito da mu daga Masar, daga ƙasar bauta.
Et lorsque ton fils t'interrogera sur ces choses, disant: Pourquoi cela? Dis-lui: Parce que le Seigneur, par sa main puissante, nous a tirés de la terre d'Égypte et de la maison de servitude,
15 Sa’ad da Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai yarda ya sallame mu ba, sai Ubangiji ya kashe dukan’ya’yan farin ƙasar Masar, na mutum da na dabba, gaba ɗaya. Domin haka nake yin hadaya ga Ubangiji da’ya’yan fari, maza, da suka fara buɗe mahaifa, amma nakan fanshi dukan’ya’yan farina maza.’
Et que, quand le Pharaon s'est endurci à ne point nous congédier, il a fait périr tout premier-né en la terre d'Égypte, depuis le premier-né des hommes jusqu'au premier-né des bestiaux. Voilà pourquoi je sacrifie au Seigneur toute tête de bétail qui a ouvert les entrailles de sa mère; et pourquoi je rachèterai tout premier-né de mes fils.
16 Za tă kuma zama alama a hannunku da kuma shaida a goshinku cewa Ubangiji ya fito da mu daga Masar da hannunsa mai iko.”
Ce sera là un signe attaché à ta main, et un mémorial devant tes yeux; car c'est par une main puissante que le Seigneur t'a tiré de l'Égypte.
17 Sa’ad da Fir’auna ya bar mutane su tafi, Allah bai bi da su a hanyar da ta bi ta iyakar Filistiyawa ba, ko da yake wannan hanya ce ta fi kusa. Gama Allah ya ce, “In suka fuskanci yaƙi, wataƙila su canja ra’ayinsu su koma Masar.”
Or, lorsque le Pharaon eut congédié le peuple, Dieu ne montra pas aux fils d'Israël la route qui passe par la terre des Philistins, quoique ce fût la plus courte. Car, dit le Seigneur, prenons garde que le peuple ne se repente, en prévoyant des combats, et qu'il ne retourne en Égypte.
18 Saboda haka Allah ya kewaye da mutanen ta hamada zuwa Jan Teku. Isra’ilawa kuwa suka fita daga Masar da shirin yaƙi.
Dieu lui fit faire un détour par le chemin qui traverse le désert jusqu'à la mer Rouge. Ce fut la cinquième génération des fils d'Israël qui sortit de la terre d'Égypte.
19 Musa ya ɗauki ƙasusuwan Yusuf tare da shi, gama Yusuf ya sa Isra’ilawa su rantse masa. Ya ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, sai ku ɗibi ƙasusuwana tare da ku daga wannan wuri.”
Moïse prit avec lui les ossements de Joseph: car celui-ci avait adjuré sous serment les fils d'Israël, et il avait dit: Le Seigneur vous visitera, et vous emporterez d'ici mes ossements avec vous.
20 Bayan sun bar Sukkot sai suka kafa sansani a Etam a bakin hamada.
Les fils d'Israël allèrent de Soccoth camper à Othom vers le désert.
21 Da rana Ubangiji yakan ja gabansu a cikin al’amudin girgije domin yă bishe su a kan hanyarsu, da dare kuma a cikin al’amudin wuta domin yă ba su haske, domin su iya tafiya dare da rana.
Dieu les guidait, le jour, par une colonne de nuée pour leur montrer la route; la nuit, par une colonne de feu.
22 Al’amudan nan biyu, na girgije da na wuta, ba su daina yi wa jama’a jagora ba.
Jamais, devant le peuple entier, la colonne de nuée ne manqua pendant le jour, ni la colonne de feu pendant la nuit.

< Fitowa 13 >