< Fitowa 12 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
UThixo wathi kuMosi lo-Aroni beseGibhithe,
2 “Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
“Inyanga le kayibe yinyanga yakuqala kini, inyanga yokuqala emnyakeni wenu.
3 Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
Tshelani bonke abomndeni ka-Israyeli ukuthi ngelanga letshumi lale inyanga indoda ngayinye kayithathele abomuzi wayo izinyane libe linye indlu ngendlu.
4 In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
Nxa abendlu bebalutshwana kakhulu ukuthi abangeke baliqede lelozinyane kababelane labomakhelwane abaseduze kwabo kusiya ngenani labo ukuthi bangaki. Kumele uphawule ukuthi kungadingeka izinyane elingakanani kusiya ngokuthi umuntu emunye angadla inyama engakanani.
5 Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
Kumele ukhethe amazinyane amaduna alomnyaka owodwa angelasici, njalo ungakhetha ezimvini loba embuzini.
6 Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
Agcine amazinyane lawo kuze kube lusuku lwetshumi lane lwenyanga, lapho isizwe sonke sako-Israyeli esizawahlaba khona nxa kuhwalala.
7 Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
Lapho-ke kuzamele bathathe igazi baligcobe emaceleni laphezulu kwemigubazi yalezozindlu abazadlela khona amazinyane.
8 A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
Ngalobobusuku kumele badle inyama eyoswe emlilweni, lesinkwa esingelamvubelo lemibhida ebabayo.
9 Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
Lingayidli inyama iluhlaza loba iphekwe ngamanzi, kodwa yoseni emlilweni konke lenhloko yakhona lamangqina kanye lezangaphakathi.
10 Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
Lingatshiyi lutho lwayo kuze kube sekuseni; kuthi nxa kukhona okuseleyo kwayo ekuseni kumele likutshise.
11 Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
Liboyidla inkalo zenu zibotshiwe, amanyathela egqokiwe lentonga zenu zisezandleni. Lidle ngokuphangisa; kuliPhasika likaThixo.
12 “A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
Ngalobobusuku ngizadabula phakathi kweGibhithe ngibulala wonke amazibulo abantu lawezinyamazana njalo ngizakwahlulela bonke onkulunkulu bamaGibhithe. Mina nginguThixo.
13 Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
Igazi lizakuba yisibonakaliso sezindlu lapho elikhona lina; kuzakuthi ngingabona igazi ngedlule kini. Akulasijeziso esibhidlizayo esizalithinta lina nxa sengichitha iGibhithe.
14 “Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
Leli akube lilanga lesikhumbuzo, kuthi zonke izizukulwane ezizayo ziligcine ngomkhosi omkhulu kuThixo, kube yisimiso sanini lanini.
15 Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
Okwensuku eziyisikhombisa kumele lidle isinkwa esingelamvubelo. Ngelanga lakuqala khuphani imvubelo ezindlini zenu, kuthi lowo odla loba yini elemvubelo ngelanga lakuqala kusiya kwelesikhombisa kumele akhutshwe ko-Israyeli.
16 A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
Ngosuku lwakuqala lenze umbuthano ongcwele, liphinde omunye ngosuku lwesikhombisa. Lingenzi msebenzi ngamalanga lawa ngaphandle kokulungisa ukudla kwabantu, yikho kodwa elingakwenza.
17 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
Gcinani uMkhosi weSinkwa esingelaMvubelo ngoba kwakulilanga engehlukanisa ngalo amaviyo enu eGibhithe. Gcinani lelilanga njengesimiso sanini lanini kuzizukulwane ezizayo.
18 A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
Ngenyanga yakuqala kumele lidle isinkwa esingelamvubelo, kusukela kusihlwa ngelanga letshumi lane kuze kube kusihlwa ngelanga lamatshumi amabili lanye.
19 Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
Okwensuku eziyisikhombisa akumelanga kutholakale imvubelo ezindlini zenu. Akuthi lowo odla loba yini elemvubelo asuswe phakathi kwabantu bako-Israyeli, loba engowezizweni kumbe owosendo lwenu.
20 Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
Lingadli lutho olufakwe imvubelo. Loba kungaphi elihlala khona libokudla isinkwa esingelamvubelo.”
21 Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
Ngakho uMosi wasebiza bonke abadala bako-Israyeli wathi kubo, “Hambani khona manje liyokhetha amazinyane ezindlu zenu lihlabe izinyane lePhasika.
22 Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
Lithathe ilixha lehisophi liyigxamuze emganwini olegazi beselithatha elinye igazi liligcobe phezulu lakunxa zonke zomgubazi. Akungabikhona lamunye wenu ozaphuma emnyango wendlu yakhe kuze kuse.
23 Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
Lapho uThixo edabula phakathi kwelizwe ebulala amaGibhithe uzalibona igazi phezulu lemaceleni omgubazi, aceze awedlule lowomnyango angamvumeli umbhubhisi ukungena endlini alibulale.
24 “Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
Lalelani imilayo le njengezimiso zaphakade kini lasezizukulwaneni zenu.
25 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
Nxa lingangena elizweni uThixo azalinika lona njengokuthembisa kwakhe, liwugcine umkhosi lo.
26 Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
Nxa abantwabenu belibuza besithi, ‘Umkhosi lo ngowani?’
27 Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
libatshele lithi, ‘UliPhasika lomhlatshelo kaThixo owadlula eceza izindlu zabako-Israyeli eGibhithe, waphephisa imizi yethu mhla egadla amaGibhithe.’” Khonapho abantu bakhothama bakhonza.
28 Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
Abako-Israyeli bakwenza lokho uThixo akuyala uMosi lo-Aroni.
29 Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
Phakathi kobusuku uThixo wawagongoda wonke amazibulo eGibhithe, kusukela ezibulweni likaFaro owayesesihlalweni sobukhosi kusiya ezibulweni lesibotshwa esasisentolongweni, kanye lamazibulo ezifuyo.
30 Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
UFaro lezikhulu zakhe zonke lawo wonke amaGibhithe bavuka ebusuku basiqhinqa isililo esikhulu eGibhithe ngoba kungekho ndlu layinye lapho okwakungafiwanga khona.
31 A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
Ebusuku uFaro wabiza uMosi lo-Aroni wathi, “Hambani! Sukani ebantwini bami, lina labako-Israyeli. Hambani liyekhonza uThixo njengokucela kwenu.
32 Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
Thathani imihlambi yenu, njengokutsho kwenu lihambe. Njalo lingibusise.”
33 Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
AmaGibhithe akhuthaza ukuthi baphangise baphume elizweni. Bathi, “Engxenye singafa sonke!”
34 Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
Ngakho abantu bathatha inhlama yabo yesinkwa ingakafakwa mvubelo bayithwala emahlombe ngemiganu yokuvubela igoqelwe ngamalembu.
35 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
Abako-Israyeli benza lokho uMosi abayala khona, bacela kumaGibhithe izinto ezenziwe ngesiliva langegolide kanye lezigqoko.
36 Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
UThixo wenza amaGibhithe aba lomusa abapha konke abakucelayo. Ngakho bawemuka impahla ezinengi amaGibhithe.
37 Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
Uhambo lwabako-Israyeli lwasukela eRamesesi baqonda eSukhothi. Kwakulamadoda azinkulungwane ezingamakhulu ayisithupha ehamba ngenyawo ngaphandle kwabesifazane labantwana.
38 Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
Abanye abantu abanengi bahamba labo kanye lemihlambi eminengi yezifuyo, izimvu lenkomo.
39 Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
Inhlama abaphuma layo eGibhithe bapheka ngayo isinkwa esingelamvubelo. Inhlama leyo yayingelamvubelo ngoba basuka eGibhithe sebexotshwa abazabe besaba lesikhathi sokuzilungisela umphako.
40 Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
Abako-Israyeli babehlale eGibhithe okweminyaka engamakhulu amane lamatshumi amathathu.
41 A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
Ekupheleni kwaleyominyaka engamakhulu amane lamatshumi amathathu kungeqanga suku wonke amaviyo kaThixo asuka eGibhithe.
42 Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
Kwathi ngoba uThixo walinda ngalobobusuku esakhupha abako-Israyeli eGibhithe, yikho-ke labo abako-Israyeli bonke kumele bawugcine umlindo lo behlonipha uThixo kuzozonke izizukulwane ezizayo.
43 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
UThixo wathi kuMosi lo-Aroni, “Nansi imilayo yePhasika: Akungabi lamuntu wezizweni olidlayo.
44 Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
Isigqili esithengwe ngemali singalidla nxa sesisokile,
45 amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
kodwa isihambi sezizweni lesisebenzi esiqhatshiweyo kabavunyelwa ukulidla.
46 “Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
Kalidlelwe endlini eyodwa, kungabi lanyama ephumela phandle kwendlu. Akungabi lathambo elephulwayo.
47 Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
Isizwe sonke sako-Israyeli kumele siwugcine lumkhosi.
48 “Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
Owezizweni ohlala phakathi kwenu nxa efuna ukulidla iPhasika likaThixo kasoke bonke abesilisa abahlala endlini yakhe. Lapho-ke usengahlanganyela adle njengomunye wenzalo yalelolizwe. Owesilisa ongasokwanga kangalidli.
49 Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
Umthetho lo ugoqela bonke abantu, abayinzalo yakini labezizweni abahlala phakathi kwenu.”
50 Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
Bonke abako-Israyeli benza khona lokhu uThixo ayekulaye uMosi lo-Aroni.
51 A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.
Njalo ngalelolanga uThixo wakhupha abako-Israyeli eGibhithe ngamaviyo abo.

< Fitowa 12 >