< Fitowa 12 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
Et le Seigneur parla à Moïse et à son frère, en la terre d'Égypte, disant:
2 “Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
Cette lune est pour vous le commencement des lunes, la première des lunes de l'année.
3 Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
Parle à toute la synagogue des fils d'Israël, disant: Que le dixième jour de cette lune chacun de vous prenne une tête de son bétail dans sa maison paternelle; chacun une victime par maison.
4 In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
Que ceux qui sont en leurs maisons trop peu nombreux pour consommer une victime, s'associent à leurs plus proches voisins, selon le nombre des âmes, afin de compléter le nombre nécessaire.
5 Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
La victime sera sans tache, mâle et d'un an; vous la prendrez parmi les agneaux et les chevreaux.
6 Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
Vous la garderez jusqu'au quatorzième jour de la lune, et sur le soir, chez tout le peuple des fils d'Israël, on l'égorgera.
7 Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
Chacun prendra de son sang, et en mettra sur les deux montants de la porte et sur le seuil de la maison en laquelle il l'aura mangée.
8 A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
Cette nuit-là on mangera les chairs rôties au feu; l'on mangera aussi des azymes avec des laitues amères.
9 Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
Vous ne mangerez les chairs ni crues ni bouillies dans l'eau, mais seulement rôties au feu; vous mangerez la tête, les pieds et les viscères.
10 Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
Que rien n'en reste au matin; vous ne broierez pas non plus les os; et ce qui resterait au matin, vous le consumerez par le feu.
11 Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
Vous mangerez ainsi: les reins ceints, les sandales aux pieds, le bâton à la main, et vous mangerez à la hâte: c'est la pâque du Seigneur.
12 “A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
En cette nuit-là, je traverserai toute l'Égypte, je frapperai tout premier-né en la terre d'Égypte, depuis les hommes jusqu'aux bestiaux, et j'exercerai ma justice sur tous les dieux des Égyptiens, moi le Seigneur.
13 Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
Alors, le sang sera pour vous un signe sur les maisons où vous demeurez; je verrai ce sang, et je vous sauverai, et il n'y aura point parmi vous de plaie qui broie, lorsque je frapperai la terre d'Égypte.
14 “Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
Ce jour-là vous sera en souvenir, et vous le fêterez comme la fête du Seigneur en toutes vos générations; vous le fêterez, c'est une loi éternelle.
15 Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
Pendant sept jours vous mangerez des azymes, et à partir du premier, vous ferez disparaître le levain de vos demeures, quiconque mangera du levain, du premier au septième jour, cette âme sera retranchée d'Israël.
16 A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
Et le premier jour sera appelé saint, le septième jour aussi sera appelé saint par vous; vous ne ferez en ces deux jours aucune œuvre servile; vous ne ferez rien que ce qui se fait pour toute âme.
17 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
Et vous observerez ce précepte; car, en ce jour-là, je conduirai toute votre armée hors de la terre d'Égypte, et vous consacrerez ce jour-là, en toutes vos générations c'est une loi éternelle.
18 A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
À partir du soir du quatorzième jour de la première lune, vous mangerez des azymes jusqu'au soir du vingt-unième jour de la lune.
19 Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
Pendant sept jours qu'il ne se trouve pas de levain en vos demeures; quiconque mangera du pain levé, qu'il soit né dans le peuple ou étranger, cette âme sera retranchée du peuple d'Israël.
20 Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
Vous ne mangerez pas de pain levé; dans toutes vos demeures, vous mangerez des azymes.
21 Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
Et Moïse appela les anciens des fils d'Israël, et il leur dit: Séparez- vous, prenez chacun une tête de menu bétail par famille, et immolez la pâque.
22 Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
Vous prendrez une branche d'hysope, vous la baignerez dans le sang laissé près de la porte, et avec le sang vous en effleurerez le linteau et les deux montants. Chacun de vous se gardera jusqu'à l'aurore de franchir le seuil de sa maison.
23 Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
Alors, le Seigneur viendra frapper les Égyptiens; il verra le sang sur le linteau et les montants des portes, et le Seigneur passera outre; il ne permettra pas à l'exterminateur d'entrer en vos maisons pour vous frapper.
24 “Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
Ce que je viens de vous dire, vous le garderez comme loi éternelle pour vous-mêmes et pour vos descendants.
25 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
Lorsque vous serez entrés en la terre que vous donnera le Seigneur selon sa promesse, vous conserverez ce rite sacré.
26 Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
Et quand vos fils vous diront: Quel est ce sacrifice?
27 Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
Vous répondrez: C'est le sacrifice de la pâque du Seigneur, parce que lorsqu'en Égypte il a frappé les Égyptiens, il a protégé les maisons des fils d'Israël et sauvé leurs demeures. À ces mots le peuple, s'étant prosterné, adora.
28 Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
Et les fils d'Israël se séparèrent pour faire ce que le Seigneur avait prescrit à Aaron et à Moïse.
29 Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
Et, le milieu de la nuit étant venu, le Seigneur frappa tout premier-né en la terre d'Égypte, depuis le premier-né du Pharaon assis sur le trône, jusqu’au premier-né de la captive dans sa prison, et jusqu'au première des bestiaux.
30 Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
Le Pharaon se leva durant la nuit, ainsi que tous ses serviteurs, et tous les Égyptiens; il y eut un long cri en la terre d'Égypte, car il n'était pas de maison où il n'y eût un mort.
31 A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
Et le Pharaon appela, durant la nuit, Moïse et son frère, et il leur dit: Levez-vous, sortez de mon royaume avec les fils d'Israël; allez et sacrifiez au Seigneur votre Dieu, comme vous l'avez demandé.
32 Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
Emmenez vos brebis et vos bœufs, partez et bénissez-moi.
33 Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
Et les Égyptiens en toute hâte contraignaient le peuple pour le faire sortir de la contrée: Car, disaient-ils, nous allons tous périr.
34 Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
Aussitôt, le peuple prit sur ses épaules sa farine en pâte non encore levée, et ses pains enveloppés dans des vêtements.
35 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
Or, les fils d'Israël avaient exécuté l'ordre de Moïse; ils avaient demandé aux Égyptiens des vases d'argent et d’or, des vêtements.
36 Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
Le Seigneur avait fait trouver grâce au peuple devant les Égyptiens qui leur avaient tout prêté; et ainsi le peuple dépouilla les Égyptiens.
37 Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
Et les fils d'Israël partirent de Rhamessès pour Soccoth au nombre de six cent mille hommes de pied, outre les bagages.
38 Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
Et avec eux une innombrable mêlée de brebis, de bœufs et de bêtes de somme.
39 Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
Et ils firent cuire la pâte qu'ils avaient emportée d'Égypte; ils en firent des azymes cuits sous la cendre; car elle n'était pas levée, tant les Égyptiens les avaient pressés de partir; ils n'avaient donc pu différer, et ils n'avaient point préparé, de vivres pour la route.
40 Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
Or, le séjour que les fils d'Israël avaient fait tant dans la terre d'Égypte que dans celle de Chanaan, avait duré quatre cent trente ans.
41 A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
Et, après ces quatre cent trente ans, il advint que toute l'armée du Seigneur sortit de la terre d'Égypte pendant la nuit.
42 Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
Cette nuit doit être consacrée au Seigneur, comme lorsqu'il les a tirés de la terre d'Égypte; cette même nuit est à garder pour le Seigneur durant toutes les générations des fils d'Israël.
43 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
Le Seigneur dit ensuite à Moïse et à son frère: Voici la loi de la pâque: Nul étranger ne prendra part au repas pascal.
44 Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
Tout serviteur né dans la famille, tout esclave acheté à prix d'argent sera circoncis par vous; alors il y participera.
45 amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
Le passager et le mercenaire n'y prendront point part.
46 “Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
La pâque sera mangée dans les maisons, et vous ne porterez hors de la maison aucune part des chairs, et vous ne broierez pas un seul os.
47 Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
Toute la synagogue d'Israël fera ainsi.
48 “Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
Et si quelqu'un est venu vers vous comme prosélyte, pour faire la pâque du Seigneur, circoncisez tout mâle dans sa famille; alors il sera admis à la faire, et il sera comme celui qui est né dans le pays; nul incirconcis ne prendra part à la pâque.
49 Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
Il n'y aura qu'une loi, tant pour l'indigène, que pour celui qui arrivera comme prosélyte parmi vous.
50 Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
Et les fils d'Israël firent ce que le Seigneur avait prescrit pour eux à Aaron et à Moïse; ils le firent;
51 A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.
Et en ce jour-là, le Seigneur conduisit hors de la terre d'Égypte les fils d'Israël avec toute leur armée.

< Fitowa 12 >