< Fitowa 12 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
Yahweh said to Aaron and Moses/me there in Egypt,
2 “Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
“[From now on], this month [will be] the first month of the year for you.
3 Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
Tell all the Israeli people that in each family, the man who heads the family must select a lamb or a young goat for his household.
4 In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
If there are not enough people in his family to eat a whole [cooked] lamb, then his family and the family that lives next door may share one animal. Decide how many lambs you need according to the number of people in each family, and according to how much each person can eat.
5 Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
The lambs or goats that you choose must be males, one-year-old, and they must not have any defects.
6 Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
You must take [special] care of these animals until the 14th day of the month. On that day, all the Israeli people must slaughter the lambs [or goats] in the evening.
7 Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
Then they must take some of the blood [from the lambs or goats], and they must smear it on the doorposts and the (lintels/horizontal beams above the doorways) of the houses in which they will eat the meat.
8 A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
They must roast the animals immediately and eat the meat that night. They must eat it with bread that is baked without yeast and with bitter herbs.
9 Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
You must not eat any of the meat raw, and you must not boil the meat. You must roast it [whole], without cutting off the head or the legs or removing the internal parts.
10 Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
You must eat all the meat that evening; do not let any of the meat remain [to be eaten] the next morning. If any of the meat is left until the next morning, you must [completely] burn it.
11 Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
When you eat it, you must be dressed ready to travel, and you must eat it quickly. You must have your sandals on your feet and your walking stick in your hands. It will be a festival [called] Passover to [honor] me, Yahweh.
12 “A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
On that night I will go through all the country of Egypt, and I will kill all the oldest males in Egypt, both humans and animals. [By doing this] I will show that all the gods in Egypt are worthless. [I can do this], because I am Yahweh, [the all-powerful God].
13 Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
The blood [that you smear on the doorways will be a mark to indicate] the houses in which you [Israelis] live. When I see the blood, I will [ignore and] pass by those houses, and I will not harm you [Israelis who live there], when I punish the Egyptians.
14 “Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
[Each year], you must celebrate this festival on this day, to remember [what I], Yahweh, [have done for you]. In all the generations to come, [each year] you must celebrate [this festival]. [It must continue] forever.
15 Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
For seven days you must eat bread that has no yeast in it. On the first day of that week you must get rid of all the yeast that is in your houses. During those seven days, if anyone eats bread that is baked with yeast in it, [you must consider] that person to be no longer an Israeli.
16 A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
On the first day [of that week], you must (have a holy meeting/gather together to [worship] me). You must do the same thing on the seventh day. People must not work on those two days. The only work they may do is to prepare food for you to eat.
17 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
[Every year] you must keep celebrating this festival of eating bread that has no yeast in it, because it will remind you that it was on this day that I brought all your tribal groups out of Egypt. So [every year], in all the generations to come, you must celebrate this day as a festival. It must continue forever.
18 A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
In the first month of the year, on the 14th day of that month, the only bread you may eat is bread that has no yeast in it. You must keep doing that each day until the 21st day of that month. For those seven days you must not have any yeast in your house. [During that time], if anyone, either an Israeli or a foreigner, eats bread made with yeast, you must consider that person no longer to be an Israeli.
19 Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
20 Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
In your houses, do not eat anything that has yeast in it during those seven days.”
21 Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
Then Moses/I summoned all the leaders of the Israeli people. He/I said to them, “Each family should select a lamb and kill it, [in order that you may eat it to celebrate the festival that will be called] ‘Passover’.
22 Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
Let the lamb’s blood [drain into] a basin. Get a bunch/sprig of (hyssop/a very leafy plant) and dip it in the blood. Then smear some of the blood on the doorposts and the (lintels/beams above the doorways) [of your houses]. The people in each house must all stay inside the house until the next morning.
23 Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
When Yahweh goes throughout Egypt to kill the [oldest male in each] Egyptian family, he will see the blood on the (lintels/beams of your doorways), and he will [ignore and] pass by those houses. He will not allow the angel who causes people to die to enter your houses and kill [any of] your [oldest sons].
24 “Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
You and your descendants must celebrate this festival forever.
25 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
And when you arrive in the land that Yahweh will be giving to you as he promised, you must keep celebrating this ritual [every year].
26 Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
When your children ask you, ‘What does this ritual mean?’,
27 Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
you must tell them, ‘This ritual is [to remember how our ancestors] sacrificed [lambs] on the night that Yahweh’s angel passed by the houses of the Israeli people [when they were] in Egypt. He killed the [oldest males/sons in all] the Egyptian houses, but he spared [the sons in] [MTY] our houses.’” After Moses/I told them this, they all bowed their heads and worshiped [Yahweh].
28 Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
Then the Israeli people did what Yahweh had told Aaron and Moses/me [to tell them to do].
29 Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
At midnight Yahweh killed all the oldest sons of the Egyptian people, all over Egypt. That included the king’s oldest son, the oldest sons of the prisoners in the dungeon/jail, and [the oldest sons of everyone else]. He also killed the oldest males of all the Egyptians’ livestock.
30 Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
That night the king, all his officials, and [all the rest of] the Egyptian people awoke [and discovered what had happened]. They wailed loudly all over Egypt, because in every house, someone’s son had died.
31 A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
That night the king summoned Aaron and Moses/me and said, “You and all the [other] Israeli people, must leave my country [immediately]! Go and worship Yahweh, as you requested!
32 Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
Take your flocks [of sheep and goats] and herds [of cattle], and leave! And ask Yahweh to bless me, also!”
33 Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
Then the Israeli people did as Moses/I had told them. They [went to] their Egyptian [neighbors] and asked them for silver and gold jewelry and clothing.
34 Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
Yahweh caused the Egyptian people to greatly respect the [Israeli] people, so they gave them what they asked for. In that way, they carried away the wealth of the Egyptian people.
35 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
The Egyptians urged the [Israeli] people to leave their country quickly. They said, “[If you do not do that], we will all die!”
36 Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
So the [Israeli] people [prepared to leave at once]. They took the bowls in which they mixed the dough to make bread, and the dough that was in the bowls without any yeast in it, and they wrapped the bowls in their cloaks. They put the bowls on their shoulders [and left].
37 Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
The Israeli people traveled from Rameses [city] to Succoth [town]. There were about 600,000 men who went, in addition to the women and children.
38 Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
Many other people who were not Israelis went along with them. There were also livestock, the flocks [of sheep and goats] and herds [of cattle].
39 Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
On their way, they baked bread with the dough that they carried with them when they had been expelled from Egypt. The dough did not have yeast in it, because they were told to leave Egypt so quickly that they did not have enough time to get food ready to take with them, or enough time to mix yeast in the dough.
40 Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
The Israeli people had lived in Egypt 430 years.
41 A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
On the day that those 430 years ended, on that very day, all the tribes of Yahweh’s people left Egypt.
42 Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
It was a night when Yahweh (protected/guarded over) them as he brought them out of Egypt. So this same night every year is a night that is dedicated to Yahweh, a night when the Israeli people in every generation [remember how] Yahweh protected our ancestors.
43 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
Then Yahweh said this to Aaron and Moses/me: “These are my instructions about the Passover ritual: Do not let foreigners eat [the Passover meal]. But any male slaves that you have bought may eat it after you have circumcised them.
44 Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
45 amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
Do not let people who are living among you temporarily, or servants whom you have hired, eat [the Passover meal].
46 “Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
Each family must eat the Passover meal inside their own house. Do not take any of the food outside the house. And do not break any of the bones of the lamb that is sacrificed.
47 Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
All the Israeli people must celebrate this festival.
48 “Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
When someone from another country comes to live with you and wants to celebrate the Passover Festival, circumcise all the males in his household. Then they may eat the Passover meal, and you should treat those people as though they were born as Israelis. But do not allow men who have not been circumcised to eat the Passover meal.
49 Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
These rules apply to people who were born as Israelis and to foreigners who come and live among you.”
50 Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
All the Israeli people obeyed Aaron and Moses/me and did what Yahweh had commanded.
51 A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.
On that very day Yahweh brought all the tribes of the Israeli people out of Egypt.

< Fitowa 12 >