< Fitowa 12 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
Then spake Yahweh, unto Moses and unto Aaron, in the land of Egypt saying—
2 “Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
This month, is, to you, a beginning of months, —the first, it is, to you, of the months of the year.
3 Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
Speak ye unto all the assembly of Israel, saying, On the tenth of this month, then let them take to them, each man a lamb for his ancestral household, a lamb for a household.
4 In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
But if the household be too small for a lamb, then shall he and his neighbour that is near unto his house take one, according to the number of souls, —each man according to his eating, shall ye number for the lamb.
5 Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
A lamb without defect a male a year old, shall yours be, —from the sheep or from the goats, shall ye take it.
6 Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
So shall it be yours, to keep, until the fourteenth day of this month, —then shall all the convocation of the assembly of Israel slay it between the two evenings.
7 Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
And they shall take of the blood, and put upon the two door-posts and upon the upper-beam, —upon the houses wherein they are to eat it.
8 A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
Then shall they eat the flesh, in the same night, —roast with fire, and with unleavened cakes, with bitter herbs, shall they eat it.
9 Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
Do not eat of it underdone, nor cooked by boiling in water, —but roast with fire, its head with its legs, and with its inward parts.
10 Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
And ye shall let nothing thereof remain until morning, —but that which is left remaining until morning, in the fire shall ye consume.
11 Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
And, thus, shall ye eat it, —your loins, girded, your sandals, on your feet, and, your staff, in your hand, —so shall ye eat it in haste, it is Yahweh’s, passing over.
12 “A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
I will pass along, therefore, throughout the land of Egypt this night, and will smite every firstborn in the land of Egypt, from man even to beast, —and against all the gods of Egypt, will I execute judgments—I, Yahweh.
13 Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
Then shall the blood serve you for a sign, on the houses wherein ye are, then will I behold the blood, and will pass over you, —and there shall be among you no plague to destroy, when I smite the land of Egypt.
14 “Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
So shall this day serve you for a memorial, and ye shall celebrate it, as a festival to Yahweh, —to your generations—as an age-abiding statute, shall ye celebrate it.
15 Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
Seven days, unleavened cakes, shall ye eat, surely, on the first day, shall ye put away leaven, out of your houses, —for whosoever eateth what is leavened, then shall that soul be cut off out of Israel, from the first day, unto the seventh day.
16 A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
Both on the first day, a holy convocation, and on the seventh day—a holy convocation, shall there be to you, —no work, shall be done therein, save only what must be eaten by every soul, that alone, shall be done by you.
17 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
So then ye shall observe the unleavened cakes, because on this self-same day, brought I forth your hosts out of the land of Egypt, —so then ye shall observe this day to your generations, as a statute age-abiding,
18 A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
In the first month, on the fourteenth day of the month in the evening, shall ye eat unleavened cakes, —until the one-and-twentieth day of the month in the evening,
19 Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
For seven days, leaven, shall not be found in your houses, —for, whosoever eateth what is leavened, then shall that soul be cut off out of the assembly of Israel, whether sojourner or native of the land.
20 Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
Nothing leavened, shall ye eat, —in all your dwellings, shall ye eat unleavened cakes.
21 Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
So then Moses called for all the elders of Israel, and said unto them, —Proceed and take for yourselves one of the flock according to your families, and slay the passover.
22 Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
Then shall ye take a bunch of hyssop, and dip it in the blood which is in the basin, and strike the upper beam and the two door-posts, with the blood which is in the basin, —and, ye, shall not go forth any man out of the entrance of his house, until morning,
23 Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
And Yahweh will pass along to plague the Egyptians, and when he beholdeth the blood upon the upper beam and upon the two door-posts, then will Yahweh pass over the entrance, and not suffer the destroyer to enter into your houses to inflict on you the plague.
24 “Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
And ye shall observe this thing, —for a statute to thee and to thy sons unto times age-abiding.
25 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
And so it shall come to pass when ye shall enter into the land which Yahweh will give you as he hath spoken, —and ye shall observe this service;
26 Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
and it shall come to pass that your sons shall say unto you, —What is this your service?
27 Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
Then shall ye say—A passover sacrifice, it is to Yahweh, who passed-over the houses of the sons of Israel, in Egypt, when he plagued the Egyptians but our houses, he delivered. Then did the people bend their heads and bow themselves down.
28 Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
And the sons of Israel went their way and did, —as Yahweh had commanded Moses and Aaron, so, did they.
29 Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
And it came to pass, at midnight, that Yahweh, smote every firstborn in the land of Egypt, from the firstborn of Pharaoh who sat upon his throne, unto the firstborn of the captive who was in the pit of his prison, —and every firstborn of beasts.
30 Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
Then rose up Pharaoh by night, he, and all his servants, and all the Egyptians, and there arose a great outcry throughout Egypt, —for there was not a house, where there was not one dead.
31 A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
So he called for Moses and for Aaron by night and said—Rise ye, go forth out of the midst of my people, both ye and the sons of Israel, —and go serve Yahweh according to your word;
32 Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
also, your flocks and your herds, take ye, as ye spake and go your way, —so shall ye bless, even me.
33 Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
And the Egyptians became urgent with the people, to send them in haste out of the land, —for they said—We all, are dying.
34 Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
So the people took up their dough, ere yet it was leavened, —with their kneading-bowls, bound up in their mantles on their shoulders,
35 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
And the sons of Israel, did according to the word of Moses, —and asked of the Egyptians, articles of silver and articles of gold and mantles.
36 Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
And Yahweh, gave the people favour in the eyes of the Egyptians and they gave them gladly, —so they spoiled the Egyptians.
37 Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
Then did the sons of Israel break up from Rameses, towards Succoth, —about six hundred thousand foot of men grown, besides little ones.
38 Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
Moreover also, a mixed multitude, came up with them, —flocks also, and herds, exceeding much cattle,
39 Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
Then baked they the dough which they had brought out of Egypt—into round unleavened cakes for it had not been leavened, —for they had been driven out of Egypt and could not tarry, and indeed no provisions, had they made ready for themselves.
40 Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
Now, the time during which the sons of Israel dwelt in Egypt, was four hundred and thirty years.
41 A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
And it came to pass at the end of four hundred and thirty years, yea it came to pass, on this self-same day, that all the hosts of Yahweh had come forth out of the land of Egypt.
42 Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
A night of solemn observances, it is unto Yahweh, for bringing them forth out of the land of Egypt, —this same night, pertaineth to Yahweh, for solemn observances by all the sons of Israel to their generations.
43 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
And Yahweh said unto Moses and Aaron: This, is the statute of the passover, —No stranger, shall eat thereof;
44 Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
but, every man’s servant bought with silver, —when thou hast circumcised him, then, shall he eat thereof:
45 amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
An alien or a hireling, shall not eat thereof.
46 “Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
In one house, shall it be eaten, thou shalt not take forth out of the house any of the flesh outside; and a, bone thereof, shalt thou not break.
47 Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
All the assembly of Israel, shall keep it.
48 “Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
And when there may sojourn with thee a sojourner who may wish to keep a passover to Yahweh, there must be circumcised to him every male and then, may he draw near to keep it, so shall he be as a native of the land, —but no uncircumcised male, shall eat thereof.
49 Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
One law, shall there be for the native, and for the sojourner that sojourneth in your midst.
50 Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
Thus did all the sons of Israel, —as Yahweh had commanded Moses and Aaron, so, did they.
51 A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.
And it came to pass, on this self-same day, that Yahweh brought forth the sons of Israel out of the land of Egypt, by their hosts.

< Fitowa 12 >