< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
Rəbbee Mısayk'le eyhen: – Zı fironulqayiy Misirılqa sayib balyaa g'axuvles. Mançile qiyğa mang'vee şu inçe g'avkvasınbı. Saccu avak'neva vuk'lele haa'as.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Milletık'le eyhe, adameeşeyiy yedaaşe hiqiy-allane Misirbışike nuk'raykeyiy k'ınəəğəyke hı'iyn karbı heqqecen.
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
Rəbbee məxüd ha'a, Misirbışde ulesqa millet yugda qadayle. Mısamee fironne insanaaşik'le, Misirne milletık'le geer xərna insan xhinne ats'a eyxhe.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
Mısee fironuk'le eyhen: – Rəbbe inəxüdud eyhe: «Xəm sura vuxhamee, Zı Misirne yı'q'neençe ılğeç'es.
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
Taxtıl gyu'arasde fironne ts'erriyne duxayle girğıl, suk giviyxərne g'ayeyne yı'q'əl giy'ırne nukarne duxalqamee, gırgıng'un ts'eppiyn dixbı hapt'asınbı. Həyvanaaşinıd çikana ts'ettiyn balabı hatt'asınbı.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
Misirvolle xədın geşşuy ixhes. Məxdın geşşuy mankilqameeyid ıxha deşdiy, mançile qiyğad mısacad ixhes deş.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
İzrailybışilqayiy cone çavra-vəq'əlqa xvaayib gihivxhas deş». Mançike şok'le ats'axhxhesın Rəbbee İzrailybıyiy Misirbı nəxübiy sana-sang'uke curav'u.
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
Yiğın insanar zasqa abı, yizde g'elybışeeqa qutyopk'ul eyhesın: «Ğunar hoora, vaqa qihna hoyharan gırgın milletıd hooracen!» Mançile qiyğa zı əlyhəəsda. Manıd uvhu, Mısa qəlın qek'a fironusse qığeç'ena.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
Rəbbee Mısayk'le eyhen: – Zasse Misir geed əlaamatbı hagvas əxecenva, fironee şol k'ırı alixhxhes deş.
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
Mıseeyiy Harunee man gırgın əlaamatbı fironuk'le hagveyid, Rəbbee fironuke hı't'iy hı'ı, mang'vee İzrailybı cune ölkeençe g'avku deş.

< Fitowa 11 >