< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
Gospod je rekel Mojzesu: »Še eno nadlogo več bom privedel nad faraona in nad Egipt, potem vam bo pustil oditi. Ko vam bo pustil oditi, vas bo zagotovo vse skupaj sunil od tod.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Govori torej v ušesa ljudstvu in naj si vsak mož izposodi od svojega soseda in vsaka ženska od svoje sosede dragocenosti iz srebra in dragocenosti iz zlata.«
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
Gospod je dal ljudstvu naklonjenost v očeh Egipčanov. Poleg tega je bil človek Mojzes zelo velik v egiptovski deželi, v očeh faraonovih služabnikov in v očeh ljudstva.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
Mojzes je rekel: »Tako govori Gospod: ›Okoli polnoči bom odšel ven, v sredo Egipta.
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
Vsi prvorojenci v egiptovski deželi bodo umrli, od faraonovega prvorojenca, ki sedi na njegovem prestolu, celo do prvorojenca dekle, ki je za mlinom in vse prvorojeno od živali.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
Veliko vpitje bo po vsej egiptovski deželi, kot takšnega tam ni bilo niti ne bo več podobnega temu.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
Toda zoper kateregakoli izmed Izraelovih otrok niti pes ne bo premaknil svojega jezika, zoper človeka ali žival, da boste lahko vedeli, kako Gospod postavlja razliko med Egipčani in Izraelom.‹
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
Vsi ti tvoji služabniki bodo prišli dol k meni in se mi priklonili, rekoč: ›Pojdi ven ti in vse ljudstvo, ki ti sledi.‹ In potem bom šel ven.« In od faraona je odšel v veliki jezi.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
Gospod je rekel Mojzesu: »Faraon vama ne bo prisluhnil, da bodo moji čudeži lahko pomnoženi v egiptovski deželi.«
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
Mojzes in Aron sta vse te čudeže storila pred faraonom, Gospod pa je zakrknil faraonovo srce, tako da ta ne bi pustil Izraelovih otrok oditi ven iz svoje dežele.

< Fitowa 11 >