< Fitowa 11 >
1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
Yahweh dit à Moïse: « Je ferai venir encore une seule plaie sur Pharaon et sur l’Égypte et, après cela, il vous laissera partir d’ici; et lorsqu’il vous laissera aller tout à fait, il vous chassera même d’ici.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Parle donc au peuple pour que chaque homme demande à son voisin et chaque femme à sa voisine des objets d’argent et des objets d’or. »
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
Et Yahweh fit trouver faveur au peuple aux yeux des Égyptiens; Moïse lui-même était très considéré dans le pays d’Égypte aux yeux des serviteurs de Pharaon et aux yeux du peuple.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
Moïse dit: « Ainsi parle Yahweh: Au milieu de la nuit je passerai au travers de l’Égypte;
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
et tout premier-né dans le pays d’Égypte mourra, depuis le premier-né de Pharaon assis sur son trône, jusqu’au premier-né de la servante qui est derrière la meule, et tout premier-né du bétail.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
Il y aura dans tout le pays d’Égypte une grande clameur, telle qu’il n’y en a pas eu et qu’il n’y en aura plus de semblable.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
Mais parmi tous les enfants d’Israël, personne, depuis les hommes jusqu’aux animaux, pas même un chien, ne remuera sa langue, afin que vous sachiez quelle différence Yahweh fait entre l’Égypte et Israël.
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
Alors tous tes serviteurs qui sont ici descendront vers moi et se prosterneront devant moi, en disant: Sors, toi et tout le peuple qui est à ta suite! Après quoi, je sortirai. » Et Moïse sortit de chez Pharaon en grande colère.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
Yahweh dit à Moïse: « Pharaon ne vous écoutera point, afin que mes prodiges se multiplient dans le pays d’Égypte. »
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
Moïse et Aaron opérèrent tous ces prodiges devant Pharaon, et Yahweh endurcit le cœur de Pharaon, et il ne laissa pas aller les enfants d’Israël hors de son pays.