< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
And Jehovah saith unto Moses, 'One plague more I do bring in on Pharaoh, and on Egypt, afterwards he doth send you away from this; when he is sending you away, he surely casteth you out altogether from this [place];
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
speak, I pray thee, in the ears of the people, and they ask — each man from his neighbour, and each woman from her neighbour, vessels of silver, and vessels of gold.'
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
And Jehovah giveth the grace of the people in the eyes of the Egyptians; also the man Moses [is] very great in the land of Egypt, in the eyes of the servants of Pharaoh, and in the eyes of the people.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
And Moses saith, 'Thus said Jehovah, About midnight I am going out into the midst of Egypt,
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
and every first-born in the land of Egypt hath died, from the first-born of Pharaoh who is sitting on his throne, unto the first-born of the maid-servant who [is] behind the millstones, and all the first-born of beasts;
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
and there hath been a great cry in all the land of Egypt, such as there hath not been, and such as there is not again.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
'And against all the sons of Israel a dog sharpeneth not its tongue, from man even unto beast, so that ye know that Jehovah doth make a separation between the Egyptians and Israel;
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
and all these thy servants have come down unto me, and bowed themselves to me, saying, Go out, thou and all the people who [are] at thy feet; and afterwards I do go out;' — and he goeth out from Pharaoh in the heat of anger.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
And Jehovah saith unto Moses, 'Pharaoh doth not hearken unto you, so as to multiply My wonders in the land of Egypt;'
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
and Moses and Aaron have done all these wonders before Pharaoh, and Jehovah strengtheneth Pharaoh's heart, and he hath not sent the sons of Israel out of his land.

< Fitowa 11 >