< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
And the Lord seide to Moises, Yit Y schal touche Farao and Egipt with o veniaunce, and after these thingis he schal delyuere you, and schal constreyne you to go out.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Therfor thou schalt seie to al the puple, that a man axe of his freend, and a womman of hir neiyboresse, silueren vessels and goldun, and clothis;
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
forsothe the Lord schal yyue grace to his puple bifor Egipcians. And Moises was a ful greet man in the lond of Egipt, bifore the seruauntis of Farao and al the puple;
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
and he seide, The Lord seith these thingis, At mydnyyt Y schal entre in to Egipt;
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
and ech firste gendrid thing in the lond of Egipcians schal die, fro the firste gendrid of Farao, that sittith in the trone of hym, til to the firste gendrid of the handmayde, which is at the querne; and alle the firste gendrid of beestis schulen die;
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
and greet cry schal be in al the lond of Egipt, which maner cry was not bifore, nether schal be aftirward.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
Forsothe at alle the children of Israel a dogge schal not make priuy noise, fro man til to beeste; that ye wite bi how greet myracle the Lord departith Egipcians and Israel.
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
And alle these thi seruauntis schulen come doun to me, and thei schulen preye me, and schulen seie, Go out thou, and al the puple which is suget to thee; aftir these thingis we schulen go out.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
And Moyses was ful wrooth, and yede out fro Farao. Forsothe the Lord seide to Moises, Farao schal not here you, that many signes be maad in the lond of Egipt.
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
Sotheli Moises and Aaron maden alle signes and wondris, that ben writun, bifor Farao; and the Lord made hard the herte of Farao, nether he delyuerede the sones of Israel fro his lond.

< Fitowa 11 >