< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
Then Yahweh said to Moses, “There is still one more plague that I will bring on Pharaoh and Egypt. After that, he will let you go from here. When he finally lets you go, he will drive you away completely.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Instruct the people that every man and woman is to ask of his or her neighbor for articles of silver and articles of gold.”
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
Now Yahweh had made the Egyptians eager to please the Israelites. Moreover, the man Moses was very impressive in the sight of Pharaoh's servants and the people of Egypt.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
Moses said, “Yahweh says this: 'About midnight I will go throughout Egypt.
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
All the firstborn in the land of Egypt will die, from the firstborn of Pharaoh, who sits on his throne, to the firstborn of the slave girl who is behind the handmill grinding it, and to all the firstborn of the cattle.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
Then there will be a great wailing throughout all the land of Egypt, such as has never been nor ever will be again.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
But not even a dog will bark against any of the people of Israel, against either man or beast. In this way you will know that I am treating the Egyptians and the Israelites differently.'
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
All these servants of yours, Pharaoh, will come down to me and bow down to me. They will say, 'Go, you and all the people who follow you!' After that I will go out.” Then he went out from Pharaoh in great anger.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
Yahweh said to Moses, “Pharaoh will not listen to you. This is so that I will do many amazing things in the land of Egypt.”
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
Moses and Aaron did all these wonders before Pharaoh. But Yahweh hardened Pharaoh's heart, and Pharaoh did not let the people of Israel go out of his land.

< Fitowa 11 >