< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
Then Yahweh said to Moses/me, “I will cause one more disaster to strike the king of Egypt and all his people [MTY]. After that, he will let you leave. In fact, he will expel you all.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
So now speak to all the [Israeli] people. Tell them to ask all their [Egyptian] neighbors, both men and women, to give them some silver and gold jewelry.”
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
Yahweh made the Egyptians highly respect the Israeli people. In particular, the Egyptian officials and all [the rest of] the people considered Moses/me to be a very great man.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
Then Moses/I [went to the king and] said, “This is what Yahweh says: ‘About midnight [tonight] I will go throughout Egypt,
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
and I will cause all the firstborn/oldest [sons] to die. That will include your oldest son, the oldest sons of the slave women who grind grain, [and the oldest sons of everyone else]. I will also kill the oldest males of the Egyptians’ livestock.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
When that happens, people all over Egypt will wail loudly. They have never wailed like that before, and they will never wail like that again.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
But among the Israeli people [it will be so quiet that] not even a dog will bark! Then you will know for sure that I, Yahweh, distinguish [how I act toward] the Egyptians and [how I act toward] the Israeli people.
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
Then all these officials of yours will come and bow down before me and will say, “Please get out [of Egypt], you and all the Israeli people!”’ After that, I will leave Egypt!” [After Moses/I said that], he/I very angrily left the king.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
Then Yahweh said to Moses/me, “The king will not pay any attention to what you say. The result will be that I will perform more plagues in the land of Egypt.”
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
Aaron and Moses/I performed all these miracles in front of the king, but Yahweh made the king stubborn, and he did not let the Israeli people leave his country.

< Fitowa 11 >