< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
And he said Yahweh to Moses yet a plague one I will bring on Pharaoh and on Egypt after thus he will let go you from here when lets [you] go he completely completely he will drive out you from here.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Speak please in [the] ears of the people so they may ask everyone [masc] - from with neighbor [masc] his and everyone [fem] from with neighbor [fem] her articles of silver and articles of gold.
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
And he gave Yahweh [the] favor of the people in [the] eyes of Egypt also - the man Moses [was] great very in [the] land of Egypt in [the] eyes of [the] servants of Pharaoh and in [the] eyes of the people.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
And he said Moses thus he says Yahweh about [the] middle of the night I [am] about to go out in [the] midst of Egypt.
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
And he will die every firstborn in [the] land of Egypt from [the] firstborn of Pharaoh who sits on throne his unto [the] firstborn of the maidservant who [is] behind the hand-mill and every firstborn of livestock.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
And it will be a cry great in all [the] land of Egypt which like it not it has occurred and like it not it will repeat.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
And to all - [the] people of Israel not it will sharpen a dog tongue its to from a human and unto livestock so that you may know! that he separates Yahweh between Egypt and between Israel.
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
And they will come down all servants your these to me and they will bow down to me saying go out you and all the people which [is] at feet your and after thus I will go out and he went out from with Pharaoh with heat of anger.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
And he said Yahweh to Moses not he will listen to you Pharaoh so as to be many wonders my in [the] land of Egypt.
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
And Moses and Aaron they did all the wonders these before Pharaoh and he made strong Yahweh [the] heart of Pharaoh and not he let go [the] people of Israel from land his.

< Fitowa 11 >