< Fitowa 11 >
1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
“Još ću samo jednom nedaćom udariti faraona i Egipat”, reče Jahve Mojsiju. “Poslije toga pustit će vas odavde. I više: sam će vas odavde potjerati.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Kaži svijetu neka svaki čovjek ište od svoga susjeda i svaka žena od svoje susjede srebrnih i zlatnih dragocjenosti.”
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
Jahve učini te Egipćani bijahu naklonjeni narodu. Sam Mojsije postane vrlo uvažen u egipatskoj zemlji, u očima faraonovih službenika i u očima naroda.
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
A onda Mojsije navijesti: “Ovako poručuje Jahve: 'O ponoći proći ću Egiptom.
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
Svaki će prvorođenac u egipatskoj zemlji umrijeti, od prvorođenca faraonova, koji bi imao sjediti na njegovu prijestolju, do prvorođenca ropkinje koja se nalazi uz mlinski kamen; a uginut će i sve prvine od stoke.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
U svoj će zemlji egipatskoj nastati veliki jauk, kakva nije bilo niti će kad poslije biti.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
Među Izraelcima ni pas neće zalajati na živo stvorenje: ni na čovjeka ni na životinju.' Po tome ćete znati da Jahve luči Izraelca od Egipćanina.
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
Onda će svi ovi tvoji dvorani k meni doći, preda me se baciti i vikati: Nosi se i ti i sav puk koji za tobom ide! Poslije toga ću otići.” I gnjevan ode od faraona.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
“Neće vas faraon poslušati”, reče Jahve Mojsiju, “a to da bi se umnožila moja znamenja u zemlji egipatskoj.”
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
Mojsije i Aron izveli su sva ta znamenja pred faraonom, ali je Jahve okorio srce faraonu, tako te on nije puštao Izraelaca da odu iz njegove zemlje.