< Fitowa 10 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
INkosi yasisithi kuMozisi: Yana kuFaro, ngoba mina ngenze inhliziyo yakhe yaba nzima lenhliziyo yenceku zakhe, ukuze ngenze lezizibonakaliso zami phambi kwakhe,
2 don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
lokuthi ulandise endlebeni zendodana yakho lendodana yendodana yakho ukuthi ngenze kabuhlungu kumaGibhithe lezibonakaliso zami engizenze phakathi kwawo, ukuze lazi ukuthi ngiyiNkosi.
3 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
UMozisi loAroni basebesiya kuFaro, bathi kuye: Itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu wamaHebheru, ithi: Koze kube nini usala ukuzithoba phambi kwami? Yekela isizwe sami sihambe, bangikhonze.
4 In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
Ngoba uba usala ukuyekela isizwe sami sihambe, khangela, kusasa ngizaletha isikhonyane emngceleni wakho,
5 Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
njalo sizasibekela ubuso bomhlaba ukuze ungawuboni umhlaba, sizakudla insalela yokwaphephayo, okwalisalelayo esiqhothweni, sidle sonke isihlahla esikhulela wena ensimini.
6 Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
Sizagcwalisa izindlu zakho lezindlu zezinceku zakho zonke lezindlu zawo wonke amaGibhithe, oyihlo abangazanga basibone laboyise baboyihlo, kusukela ngosuku ababakhona emhlabeni kuze kube lamuhla. Wasetshibilika, waphuma kuFaro.
7 Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
Lenceku zikaFaro zathi kuye: Koze kube nini lo esiba ngumjibila kithi? Yekela amadoda ahambe, akhonze iNkosi uNkulunkulu wawo; kawukazi yini ukuthi iGibhithe isichithekile?
8 Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
UMozisi loAroni babuyiselwa kuFaro; wasesithi kubo: Hambani likhonze iNkosi uNkulunkulu wenu. Ngobani kanye labo abazahamba?
9 Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
UMozisi wasesithi: Sizahamba labatsha bethu labadala bethu, lamadodana ethu lamadodakazi ethu, lezimvu zethu lenkomo zethu sizahamba, ngoba silomkhosi weNkosi.
10 Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
Wasesithi kubo: INkosi ibe lani ngokunjalo, njengoba ngizaliyekela lihambe labantwanyana benu! Bonani ngoba kulokubi phambi kwenu.
11 Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
Kungabi njalo! Hambani khathesi, madoda, liyikhonze iNkosi, ngoba yikho elikudingayo. Basebebaxotsha ebusweni bukaFaro.
12 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
INkosi yasisithi kuMozisi: Yelula isandla sakho phezu kwelizwe leGibhithe, ngenxa yesikhonyane, ukuze senyukele phezu kwelizwe leGibhithe, sidle wonke umbhida welizwe lakho konke isiqhotho esikutshiyileyo.
13 Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
UMozisi waseyelula intonga yakhe phezu kwelizwe leGibhithe; iNkosi yasiqhuba umoya wempumalanga elizweni, lonke lolosuku lobusuku bonke; kwasekusithi ekuseni, umoya wempumalanga wenyusa isikhonyane.
14 suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
Isikhonyane sasesisenyukela phezu kwelizwe lonke leGibhithe, sehlela emngceleni wonke weGibhithe, esinzima kakhulu. Phambi kwaso akuzange kube khona isikhonyane esinjalo njengaso, futhi kakuyikuba khona esinjalo emva kwaso.
15 Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
Ngoba sasibekela ubuso belizwe lonke, kwaze kwafiphazwa ilizwe; sadla wonke umbhida welizwe laso sonke isithelo sezihlahla isiqhotho esasitshiyayo; kakusalanga lutho oluluhlaza esihlahleni, lombhida weganga, elizweni lonke leGibhithe.
16 Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
UFaro wasephangisa ukubabiza oMozisi loAroni, wathi: Ngonile eNkosini uNkulunkulu wenu lakini.
17 Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
Khathesi-ke ake lithethelele isono sami okwalesisikhathi kuphela, liyincenge iNkosi uNkulunkulu wenu ukuthi isuse kimi lokhu ukufa kuphela.
18 Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
Wasephuma kuFaro, wayincenga iNkosi.
19 Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
INkosi yasiphendula umoya wentshonalanga olamandla kakhulu owenyusa isikhonyane, wasiphosela oLwandle oluBomvu; kakusalanga sikhonyane lesisodwa kuwo wonke umngcele weGibhithe.
20 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
Kodwa iNkosi yayenza lukhuni inhliziyo kaFaro, kazabayekela abantwana bakoIsrayeli bahambe.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
INkosi yasisithi kuMozisi: Yelulela isandla sakho emazulwini, ukuze kube khona umnyama phezu kwelizwe leGibhithe, ngitsho umnyama ophumputhekayo.
22 Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
UMozisi waseselulela isandla sakhe emazulwini; kwasekusiba khona umnyama wobumnyama elizweni lonke leGibhithe insuku ezintathu.
23 Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
Kababonananga, futhi kakusukumanga muntu endaweni yakhe okwensuku ezintathu; kodwa kubo bonke abantwana bakoIsrayeli kwakukhona ukukhanya emizini yabo.
24 Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
UFaro wasembiza uMozisi wathi: Hambani likhonze iNkosi, kuphela izimvu zenu lenkomo zenu kuzagcinwa, labantwanyana benu bazahamba lani.
25 Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
Kodwa uMozisi wathi: Lawe ubonika imihlatshelo leminikelo yokutshiswa ezandleni zethu, esizayenzela iNkosi uNkulunkulu wethu.
26 Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
Njalo lezifuyo zethu zizahamba kanye lathi, kakuyikusala emuva isondo; ngoba sizathatha kuzo ukukhonza iNkosi uNkulunkulu wethu, ngoba kasikwazi esizakhonza ngakho iNkosi size sifike khona.
27 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
Kodwa iNkosi yenza lukhuni inhliziyo kaFaro, njalo kafunanga ukubayekela bahambe.
28 Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
UFaro wasesithi kuye: Suka kimi, uziqaphele, ungaboni ubuso bami futhi; ngoba mhla ubona ubuso bami uzakufa.
29 Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”
UMozisi wasesithi: Ukhulume ngokuqonda, kangisayikubona futhi ubuso bakho.

< Fitowa 10 >