< Fitowa 10 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
Et le Seigneur dit à Moïse: Entre auprès de Pharaon; car c’est moi qui ai endurci son cœur et celui de ses serviteurs, afin que je fasse sur lui ces signes de ma puissance,
2 don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
Et que tu racontes aux oreilles de ton fils et de tes neveux, combien de fois j’ai brisé les Egyptiens et j’ai fait mes signes au milieu d’eux, et que vous sachiez que je suis le Seigneur.
3 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
Moïse et Aaron entrèrent donc auprès de Pharaon, et lui dirent: Voici ce que dit le Seigneur Dieu des Hébreux: Jusqu’à quand ne voudras-tu pas te soumettre à moi? Laisse aller mon peuple, afin qu’il me sacrifie.
4 In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
Que si tu résistes encore, et si tu ne veux pas le laisser aller, voilà que moi, je ferai venir demain des sauterelles dans tes confins;
5 Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
Pour qu’elles couvrent la surface de la terre; en sorte qu’il n’en paraisse rien; mais que ce qui sera resté après la grêle, soit mangé; car elles rongeront tous les arbres qui poussent dans les champs.
6 Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
Et elles rempliront tes maisons, et celles de tes serviteurs et de tous les Egyptiens; ni tes pères, ni tes aïeux n’en ont vu autant depuis qu’ils sont nés sur la terre, jusqu’au présent jour. Et il se retira, et il sortit d’avec Pharaon.
7 Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
Mais les serviteurs de Pharaon lui dirent: Jusqu’à quand souffrirons-nous ce scandale? Laissez aller ces hommes, afin qu’ils sacrifient au Seigneur leur Dieu: ne voyez-vous pas que l’Egypte est perdue?
8 Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
Ils rappelèrent donc Moïse et Aaron auprès de Pharaon, qui leur dit: Allez, sacrifiez au Seigneur votre Dieu: qui sont ceux qui doivent y aller?
9 Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
Moïse répondit: Nous irons avec nos petits enfants et nos vieillards, avec nos fils et nos filles, avec nos brebis et notre gros bétail; car c’est une solennité du Seigneur notre Dieu.
10 Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
Et Pharaon repartit: Que le Seigneur soit avec vous de la même manière que moi, je vous laisserai aller, vous et vos petits enfants: qui doute que vous ne formiez de très mauvais desseins?
11 Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
Non, il n’en sera pas ainsi; mais allez, vous autres hommes seulement, et sacrifiez au Seigneur; car c’est ce que vous-mêmes avez demandé. Et aussitôt ils furent renvoyés de la présence de Pharaon.
12 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
Mais le Seigneur dit à Moïse: Etends ta main sur la terre d’Egypte vers les sauterelles, afin qu’elles montent sur la terre, et qu’elles dévorent toute l’herbe qui est restée après la grêle.
13 Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
Et Moïse étendit sa verge sur la terre d’Egypte, et le Seigneur fit venir un vent brûlant, qui souffla tout ce jour-là et toute la nuit; et, le matin venu, le vent brûlant fit lever les sauterelles;
14 suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
Qui montèrent sur toute la terre d’Egypte; et elles s’arrêtèrent dans tous les confins des Egyptiens en nombre infini, telles qu’avant ce temps-là il n’y en avait pas eu, et qu’à l’avenir il ne doit pas y en avoir
15 Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
Ainsi, elles couvrirent la surface entière de la terre, ravageant tout. Toute l’herbe de la terre fut donc dévorée, et tout ce qui se trouva de fruits sur les arbres, fruits que la grêle avait laissés; de sorte qu’il ne resta absolument rien de vert sur les arbres ni dans les herbes de la terre, dans toute l’Egypte.
16 Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
C’est pourquoi Pharaon se hâtant appela Moïse et Aaron, et leur dit: J’ai péché contre le Seigneur votre Dieu, et contre vous.
17 Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
Mais maintenant pardonnez-moi mon péché encore cette fois, et priez le Seigneur votre Dieu, afin qu’il retire de moi cette mort.
18 Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
Moïse donc, sorti de la présence de Pharaon, pria le Seigneur,
19 Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
Qui fit souffler de l’occident un vent très violent, qui, ayant enlevé les sauterelles, les jeta dans la mer Rouge; il n’en demeura pas même une seule dans tous les confins de l’Egypte.
20 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
Mais le Seigneur endurcit le cœur de Pharaon, et il ne laissa pas aller les enfants d’Israël.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
Alors le Seigneur dit à Moïse: Etends ta main vers le ciel, et qu’il y ait sur la terre d’Egypte des ténèbres si épaisses, qu’on puisse les toucher.
22 Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
Et Moïse étendit sa main vers le ciel, et il se forma des ténèbres horribles sur l’Egypte entière pendant trois jours.
23 Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
Personne ne vit son frère, ni ne se remua du lieu où il était: mais la lumière était partout où habitaient les enfants d’Israël.
24 Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
Alors Pharaon appela Moïse et Aaron et leur dit: Allez, sacrifiez au Seigneur: que vos brebis seulement et votre gros bétail demeurent, et que vos petits enfants aillent avec vous.
25 Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
Moïse répondit: Tu nous donneras aussi des hosties et des holocaustes que nous puissions offrir au Seigneur notre Dieu.
26 Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
Tous nos troupeaux iront avec nous, et il ne demeurera pas une corne de leurs pieds; c’est nécessaire pour le culte du Seigneur notre Dieu; d’autant plus que nous ignorons ce qui doit être immolé, jusqu’à ce que nous parvenions au lieu même.
27 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
Mais le Seigneur endurcit le cœur de Pharaon, et il ne voulut pas les laisser aller.
28 Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
Et Pharaon dit à Moïse: Retire-toi de moi, et garde-toi de voir désormais ma face: car en quelque jour que ce soit que tu paraisses de vaut moi, tu mourras.
29 Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”
Moïse répondit: Il sera fait ainsi que tu las dit, je ne verrai plus ta face.