< Fitowa 10 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
Yahvé dit à Moïse: « Va vers Pharaon, car j'ai endurci son cœur et le cœur de ses serviteurs, afin de montrer mes signes au milieu d'eux;
2 don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
et afin que tu racontes à ton fils et au fils de ton fils ce que j'ai fait à l'Égypte et les signes que j'ai accomplis au milieu d'eux, pour que tu saches que je suis Yahvé. »
3 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
Moïse et Aaron allèrent trouver Pharaon et lui dirent: « Voici ce que dit Yahvé, le Dieu des Hébreux: « Jusqu'à quand refuseras-tu de t'humilier devant moi? Laisse partir mon peuple, afin qu'il me serve.
4 In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
Ou bien, si vous refusez de laisser partir mon peuple, voici que demain je ferai venir des sauterelles dans votre pays,
5 Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
et elles couvriront la surface de la terre, de sorte qu'on ne pourra plus voir la terre. Elles mangeront le reste de ce qui s'est échappé, ce qui vous reste de la grêle, et elles mangeront tout arbre qui pousse pour vous dans les champs.
6 Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
Tes maisons seront remplies, ainsi que celles de tous tes serviteurs et de tous les Égyptiens, comme n'en ont jamais vu ni tes pères ni les pères de tes pères, depuis le jour où ils ont été sur la terre jusqu'à ce jour.'" Il se retourna, et sortit de chez Pharaon.
7 Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
Les serviteurs de Pharaon lui dirent: « Jusqu'à quand cet homme sera-t-il un piège pour nous? Laisse partir ces hommes, afin qu'ils servent Yahvé, leur Dieu. Ne sais-tu pas encore que l'Égypte est détruite? »
8 Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
Moïse et Aaron furent ramenés auprès de Pharaon, qui leur dit: « Allez, servez Yahvé votre Dieu; mais qui sont ceux qui iront? »
9 Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
Moïse dit: « Nous irons avec nos jeunes et nos vieux, nous irons avec nos fils et nos filles, avec nos brebis et nos bœufs. Nous irons avec nos fils et nos filles, avec nos brebis et nos bœufs, car nous devons faire une fête à Yahvé. »
10 Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
Il leur dit: « Que Yahvé soit avec vous si je vous laisse partir avec vos petits enfants! Voyez, le mal est clairement devant vos yeux.
11 Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
Mais non! Allez maintenant, vous qui êtes des hommes, et servez Yahvé, car c'est ce que vous voulez! ». Et ils furent chassés de la présence de Pharaon.
12 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
Yahvé dit à Moïse: « Étends ta main sur le pays d'Égypte pour les sauterelles, afin qu'elles montent sur le pays d'Égypte et mangent toutes les herbes du pays, tout ce que la grêle a laissé. »
13 Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
Moïse étendit sa verge sur le pays d'Égypte, et Yahvé fit souffler un vent d'est sur le pays tout ce jour-là et toute la nuit; et au matin, le vent d'est amena les sauterelles.
14 suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
Les sauterelles montèrent sur tout le pays d'Égypte, et se posèrent dans tout le territoire de l'Égypte. Elles étaient très nuisibles. Avant elles, il n'y avait pas eu de sauterelles comme elles, et il n'y en aura plus jamais.
15 Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
Car elles couvrirent toute la surface de la terre, au point d'obscurcir le pays, et elles mangèrent toutes les herbes du pays et tous les fruits des arbres que la grêle avait laissés. Il ne resta rien de vert, ni arbre ni herbe des champs, dans tout le pays d'Égypte.
16 Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
Pharaon appela en hâte Moïse et Aaron, et dit: « J'ai péché contre Yahvé ton Dieu et contre toi.
17 Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
Maintenant, pardonne-moi encore mon péché, et prie Yahvé ton Dieu, afin qu'il éloigne de moi cette mort. »
18 Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
Moïse sortit de chez Pharaon et pria l'Éternel.
19 Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
L'Éternel envoya un vent d'ouest très fort, qui emporta les sauterelles et les chassa dans la mer Rouge. Il ne resta pas une seule sauterelle dans tout le territoire de l'Égypte.
20 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
Mais Yahvé endurcit le cœur de Pharaon, qui ne laissa pas partir les enfants d'Israël.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
Yahvé dit à Moïse: « Étends ta main vers le ciel, afin qu'il y ait des ténèbres sur le pays d'Égypte, des ténèbres qu'on puisse sentir. »
22 Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
Moïse étendit sa main vers le ciel et il y eut une obscurité épaisse dans tout le pays d'Égypte pendant trois jours.
23 Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
On ne se voyait pas les uns les autres, et personne ne se leva de sa place pendant trois jours; mais tous les enfants d'Israël avaient de la lumière dans leurs habitations.
24 Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
Pharaon appela Moïse et dit: « Va, sers Yahvé. Laisse seulement tes brebis et tes bœufs en arrière. Laisse aussi tes petits enfants aller avec toi. »
25 Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
Moïse dit: « Tu dois aussi remettre entre nos mains des sacrifices et des holocaustes, afin que nous puissions offrir des sacrifices à Yahvé, notre Dieu.
26 Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
Notre bétail aussi partira avec nous. Pas un seul sabot ne sera laissé en arrière, car c'est de lui que nous devons prendre pour servir Yahvé notre Dieu; et nous ne savons pas avec quoi nous devons servir Yahvé, jusqu'à ce que nous y arrivions. »
27 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
Mais Yahvé endurcit le cœur de Pharaon, qui ne voulut pas les laisser partir.
28 Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
Pharaon lui dit: « Éloigne-toi de moi! Prends garde de ne plus voir mon visage, car le jour où tu verras mon visage, tu mourras! ».
29 Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”
Moïse dit: « Tu as bien parlé. Je ne verrai plus jamais ton visage. »