< Fitowa 10 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
And he said Yahweh to Moses go to Pharaoh for I I have made heavy heart his and [the] heart of servants his so as to perform I signs my these in midst his.
2 don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
And so that you may recount in [the] ears of son your and [the] son of son your how I have dealt ruthlessly with Egypt and signs my which I performed among them and you will know that I [am] Yahweh.
3 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
And he went Moses and Aaron to Pharaoh and they said to him thus he says Yahweh [the] God of the Hebrews until when? have you refused to humble yourself from before me let go people my so they may serve me.
4 In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
That except [are] refusing you to let go people my here I [am] about to bring tomorrow locust[s] in territory your.
5 Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
And it will cover [the] eye of the land and not anyone will be able to see the ground and it will eat - [the] remainder of the escaped thing which remains to you from the hail and it will eat every tree that is sprouting for you from the field.
6 Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
And they will be full houses your and [the] houses of all servants your and [the] houses of all Egypt which not they saw ancestors your and [the] ancestors of ancestors your from [the] day were they on the land until the day this and he turned and he went out from with Pharaoh.
7 Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
And they said [the] servants of Pharaoh to him until when? will he become this [man] for us a snare let go the people so they may serve Yahweh God their ¿ not yet do you know that it will perish Egypt.
8 Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
And he was brought back Moses and Aaron to Pharaoh and he said to them go serve Yahweh God your who? and who? [are] the [ones] going.
9 Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
And he said Moses with young men our and with old [men] our we will go with sons our and with daughters our with flock[s] our and with herds our we will go for festival of Yahweh [will belong] to us.
10 Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
And he said to them may he be thus Yahweh with you just as I will let go you and little one[s] your see that evil [is] before faces your.
11 Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
Not so go please the men and serve Yahweh for it you [are] requesting and someone drove out them from with [the] face of Pharaoh.
12 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
And he said Yahweh to Moses stretch out hand your over [the] land of Egypt for the locust[s] so may it come up on [the] land of Egypt so it may eat all [the] vegetation of the land all that it left over the hail.
13 Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
And he stretched out Moses staff his over [the] land of Egypt and Yahweh he drove a wind of [the] east in the land all the day that and all the night the morning it was and [the] wind of the east it carried the locust[s].
14 suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
And it came up the locust[s] on all [the] land of Egypt and it settled down in all [the] territory of Egypt heavy very before it not it had been thus locust[s] like it and after it not it will be thus.
15 Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
And it covered [the] eye of all the land and it grew dark the land and it ate all [the] vegetation of the land and all [the] fruit of the tree[s] which it had left over the hail and not it was left behind any greenery on the tree[s] and on [the] vegetation of the field in all [the] land of Egypt.
16 Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
And he hurried Pharaoh to summon Moses and Aaron and he said I have sinned to Yahweh God your and to you.
17 Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
And therefore forgive please sin my only this time and pray to Yahweh God your so may he remove from on me only the death this.
18 Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
And he went out from with Pharaoh and he prayed to Yahweh.
19 Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
And he turned Yahweh a wind west strong very and it carried away the locust[s] and it blew it [the] sea of towards reed[s] not it remained a locust one in all [the] territory of Egypt.
20 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
And he made strong Yahweh [the] heart of Pharaoh and not he let go [the] people of Israel.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
And he said Yahweh to Moses stretch out hand your to the heavens so may it be darkness over [the] land of Egypt so they may feel darkness.
22 Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
And he stretched out Moses hand his to the heavens and it was darkness of darkness in all [the] land of Egypt three days.
23 Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
Not they saw each brother his and not they rose anyone from under him three days and to all [the] people Israel it be[longed] light in dwelling places their.
24 Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
And he summoned Pharaoh Moses and he said go serve Yahweh only flock[s] your and herd[s] your it will be detained also little one[s] your it will go with you.
25 Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
And he said Moses also you you will give in hand our sacrifices and burnt offerings and we will offer [them] to Yahweh God our.
26 Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
And also livestock our it will go with us not it will remain a hoof for some of it we will take to serve Yahweh God our and we not we will know what? will we serve Yahweh until go we there.
27 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
And he made strong Yahweh [the] heart of Pharaoh and not he was willing to let go them.
28 Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
And he said to him Pharaoh go from with me take heed to yourself to may you repeat to see face my for on [the] day seeing you face my you will die.
29 Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”
And he said Moses right you have spoken not I will repeat again to see face your.

< Fitowa 10 >