< Fitowa 10 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
I řekl Hospodin Mojžíšovi: Vejdi k Faraonovi, ačkoli jsem já obtížil srdce jeho, a srdce služebníků jeho, abych učinil divy tyto své u prostřed nich;
2 don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
A abys ty vypravoval v uši synů svých i vnuků svých, co jsem učinil v Egyptě, a znamení má, kteráž jsem prokázal na nich; abyste věděli, že já jsem Hospodin.
3 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
I všel Mojžíš s Aronem k Faraonovi, a řekli jemu: Takto praví Hospodin Bůh Hebrejský: Dokavadž nechceš se ponížiti přede mnou? Propusť lid můj, ať mi slouží.
4 In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
Pakli nechceš propustiti lidu mého, aj, já uvedu zítra kobylky na krajinu tvou.
5 Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
A přikryjí svrchek země, aby jí nebylo viděti, a snědí ostatky pozůstalé, kteříž vám zanecháni jsou po krupobití; zhryzou vám také každý strom pučící se na poli.
6 Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
A naplní domy tvé, i domy všech služebníků tvých, a domy všech Egyptských; čehož neviděli otcové tvoji a otcové otců tvých, od počátku bytu svého na zemi až do dne tohoto. A odvrátiv se, vyšel od Faraona.
7 Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
Řekli pak služebníci Faraonovi k němu: Dokavadž tento bude nám osídlem? Propusť ty muže, ať slouží Hospodinu Bohu svému. Zdaž ještě nevíš, že zkažen jest Egypt?
8 Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
I zavolán jest Mojžíš s Aronem před Faraona. Jimž řekl: Jděte, služte Hospodinu Bohu svému. Kdo jsou ti, kteříž jíti mají?
9 Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
A odpověděl Mojžíš: S dítkami i s starými našimi půjdeme, s syny i s dcerami našimi, s ovcemi a s větším dobytkem naším odejdeme; nebo slavnost Hospodinovu držeti máme.
10 Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
Tedy řekl jim: Nechať jest tak Hospodin s vámi, jako já propustím vás i dítky vaše. Hleďte, nebo zlé jest před tváři vaší.
11 Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
Nebudeť tak. Jděte vy sami muži, a služte Hospodinu, nebo toho vy toliko žádáte. I vyhnáni jsou od tváři Faraonovy.
12 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
Tedy řekl Hospodin Mojžíšovi: Vztáhni ruku svou na zemi Egyptskou pro kobylky, ať vystoupí na zemi Egyptskou, a sežerou všelikou bylinu země té, cožkoli zůstalo po krupobití.
13 Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
I vztáhl Mojžíš hůl svou na zemi Egyptskou; a Hospodin uvedl vítr východní na zemi, aby vál celého toho dne a celou noc. A když bylo ráno, vítr východní přinesl kobylky.
14 suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
A vystoupily kobylky na všecku zemi Egyptskou, a připadly na všecky končiny Egyptské nesčíslně. Před těmi nebylo takových kobylek, aniž po těch takové budou.
15 Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
I přikryly veškeren svrchek země, tak že pro ně nebylo lze znáti země; a sežraly všelikou bylinu země, a všeliké ovoce na stromích, kteréž zůstalo po krupobití; a nepozůstalo nic zeleného na stromích a bylinách polních ve vší zemi Egyptské.
16 Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
Tedy Farao spěšně povolav Mojžíše s Aronem, řekl: Zhřešil jsem proti Hospodinu Bohu vašemu, i proti vám.
17 Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
Ale nyní, odpusť, prosím, hřích můj aspoň tento, a modlte se Hospodinu Bohu vašemu, ať jen tuto smrt odejme ode mne.
18 Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
Protož vyšed Mojžíš od Faraona, modlil se Hospodinu.
19 Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
I obrátil Hospodin vítr západní tuhý velmi, kterýžto zachvátiv kobylky, uvrhl je do moře Rudého, tak že nezůstalo žádné kobylky ve vší krajině Egyptské.
20 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
Ale obtížil Hospodin srdce Faraonovo, a nepropustil synů Izraelských.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
I řekl Hospodin Mojžíšovi: Vztáhni ruku svou k nebi, a bude tma na zemi Egyptské, a makati ji budou.
22 Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
I vztáhl Mojžíš ruku svou k nebi, a byla tma přehustá po vší zemi Egyptské za tři dni.
23 Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
Aniž viděl jeden druhého, a aniž kdo vstal z místa svého za tři dni; ale synové Izraelští všickni měli světlo v příbytcích svých.
24 Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
Potom povolav Farao Mojžíše, řekl: Jděte, služte Hospodinu. Toliko ovce vaše a větší dobytek váš nechať zůstane, také dítky vaše půjdou s vámi.
25 Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
Odpověděl Mojžíš: Dáš také v ruce naše oběti a zápaly, kteréž bychom obětovali Hospodinu Bohu našemu.
26 Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
A protož také dobytek náš půjde s námi, a nezůstane ani kopyta; nebo z nich vezmeme ku poctě Hospodinu Bohu našemu. My pak nevíme, čím sloužiti máme Hospodinu, dokudž nepřijdeme tam.
27 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
Zatvrdil pak Hospodin srdce Faraonovo, tak že nechtěl propustiti jich.
28 Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
I řekl mu Farao: Odejdi ode mne, a varuj se, abys více neviděl tváři mé; nebo v který den uzříš tvář mou, umřeš.
29 Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”
Odpověděl Mojžíš: Dobře jsi řekl; neuzřímť více tváři tvé.