< Fitowa 1 >
1 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
Torej to so imena Izraelovih otrok, ki so prišli v Egipt. Z Jakobom je prišel vsak mož in njegova družina.
2 Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
Ruben, Simeon, Lévi in Juda,
3 Issakar, Zebulun da Benyamin;
Isahár, Zábulon in Benjamin,
4 Dan da Naftali; Gad da Asher.
Dan in Neftáli, Gad in Aser.
5 Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
Vseh duš, ki so prišle iz Jakobovih ledij, je bilo sedemdeset duš, kajti Jožef je bil že v Egiptu.
6 Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
Jožef je umrl in vsi njegovi bratje in ves ta rod.
7 amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
Izraelovi otroci pa so bili rodovitni in obilno narasli in se namnožili in postali silno mogočni in dežela je bila napolnjena z njimi.
8 Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
Sedaj je tam vstal nov kralj nad Egiptom, ki ni poznal Jožefa.
9 Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
Svojemu ljudstvu je rekel: »Glejte, ljudstva Izraelovih otrok je več in mogočnejši so, kakor smo mi.
10 Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
Pridite, modro ravnajmo z njimi, da se ne bi namnožili in se pripeti, ko izpade kakšna vojna, da se pridružijo tudi našim sovražnikom in se borijo zoper nas in tako jih napodimo iz dežele.«
11 Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
Zato so nadnje postavili preddelavce, da jih stiskajo z njihovimi bremeni. In za faraona so gradili zakladni mesti Pitóm in Ramesés.
12 Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
Toda bolj so jih stiskali, bolj so se množili in rastli. In bili so užaloščeni zaradi Izraelovih otrok.
13 ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
Egipčani so s krutostjo Izraelove otroke prisilili, da so služili.
14 Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
Njihova življenja so zagrenili s trdim suženjstvom, z malto, z opeko in z vsemi vrstami službe na polju. Vse njihove službe, s katerimi so jih pripravili, da jim služijo, so bile s krutostjo.
15 Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
Egiptovski kralj je spregovoril hebrejskima babicama, katerih prvi je bilo ime Šifra, ime drugi pa Pua
16 “Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
in rekel: »Ko hebrejskim ženam opravljata službo babice in jih vidita na stolčkih; če je sin, potem ga ubijta, toda če je hči, potem naj živi.«
17 Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
Toda babici sta se bali Boga in nista delali, kakor jima je egiptovski kralj ukazal, temveč sta fantke rešili žive.
18 Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
Egiptovski kralj je dal poklicati babici in jima rekel: »Zakaj sta storili to stvar in fantke rešili žive?«
19 Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
Babici sta faraonu rekli: »Zato ker Hebrejke niso kakor Egipčanke, kajti one so krepke in rodijo prej ko babice pridejo k njim.«
20 Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
Zato je Bog z babicama dobro postopal in ljudstvo se je pomnožilo in postalo zelo mogočno.
21 Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
Pripetilo se je, ker sta se babici bali Boga, da jima je naredil hiši.
22 Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”
Faraon je vsemu svojemu ljudstvu zapovedal, rekoč: »Vsakega sina, ki je rojen, boste vrgli v reko, vsaka hči pa naj bo rešena živa.«