< Fitowa 1 >

1 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
And these [are] [the] names of [the] sons of Israel who went Egypt towards with Jacob everyone and household his they went.
2 Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
Reuben Simeon Levi and Judah.
3 Issakar, Zebulun da Benyamin;
Issachar Zebulun and Benjamin.
4 Dan da Naftali; Gad da Asher.
Dan and Naphtali Gad and Asher.
5 Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
And it was every person [who] came out of [the] thigh of Jacob seventy person[s] and Joseph he was in Egypt.
6 Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
And he died Joseph and all brothers his and all the generation that.
7 amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
And [the] people of Israel they were fruitful and they swarmed and they multiplied and they became mighty with muchness muchness and it was filled the land with them.
8 Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
And he arose a king new over Egypt who not he knew Joseph.
9 Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
And he said to people his here! [the] people of [the] people of Israel [is] numerous and mighty more than us.
10 Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
Give! let us deal wisely to it lest it should increase and it will be that they will happen war and it will be added also it to [those who] hate us and it will fight against us and it will go up from the land.
11 Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
And they appointed over it overseers of slave gangs so as to afflict it with forced labor their and it built cities of storage for Pharaoh Pithom and Rameses.
12 Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
And just as people afflicted it so it increased and so it spread and people felt dread because of [the] people of Israel.
13 ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
And they compelled to labor Egypt [the] people of Israel with harshness.
14 Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
And they made bitter lives their with labor hard in mortar and in bricks and in all labor in the field all labor their which they labored by them with harshness.
15 Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
And he said [the] king of Egypt to the midwives Hebrew who [the] name of the one [was] Shiphrah and [the] name of the second [was] Puah.
16 “Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
And he said when assist as midwife you the Hebrew [women] and you will look at the stones if [is] a son he and you will kill him and if [is] a daughter she and she will live.
17 Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
And they feared the midwives God and not they did just as he had spoken to them [the] king of Egypt and they let live the [male] children.
18 Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
And he summoned [the] king of Egypt the midwives and he said to them why? have you done the thing this and have you let live? the [male] children.
19 Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
And they said the midwives to Pharaoh for not [are] like the women Egyptian the Hebrew [women] that [are] vigorous they before she comes to them the midwife and they give birth.
20 Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
And he did good God to the midwives and it increased the people and they became mighty exceedingly.
21 Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
And it was that they feared the midwives God and he appointed for them households.
22 Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”
And he commanded Pharaoh to all people his saying every son born the River towards you will throw him and every daughter you will let live!

< Fitowa 1 >