< Esta 9 >
1 A rana ta goma sha uku na watan goma sha biyu, wato, watan Adar ne za a aiwatar da dokar da sarki ya umarta. A wannan rana, abokan gāban Yahudawa suka sa zuciya za su sha ƙarfinsu, amma yanzu Zerzes ya canja, Yahudawa kuma suka yi galiba a bisa waɗanda suka ƙi jininsu.
Uti tolfte månadenom, det är den månaden Adar, på trettonde dagen, hvilken Konungens ord och bud förelagt hade, att man det göra skulle; rätt uppå samma dagen, då fienderna skulle öfverfallit Judarna, vände det sig så, att Judarna skulle öfverfalla sina fiendar.
2 Yahudawa suka tattaru a cikin biranensu a dukan lardunan Sarki Zerzes don su kai wa waɗanda suka nemi a hallaka su hari. Babu wanda ya tasar musu domin mutanen dukan sauran al’ummai sun jin tsoronsu.
Så församlade Judarne sig i deras städer, i allom Konungs Ahasveros landom, att de skulle göra anfall på dem som dem ondt ämnade; och ingen kunde stå emot dem; förty deras fruktan var kommen öfver all folk.
3 Dukan sarakuna larduna, da hakimai, da gwamnoni da kuma ma’aikatan sarki suka taimaki Yahudawa, domin tsoron Mordekai ya kama su.
Och alle öfverstarna i landen, och Förstarna, och landshöfdingarna, och Konungens ämbetsmän höllo Judarna i äro; ty Mardechai fruktan kom öfver dem.
4 Mordekai babban mutum ne a fada, sunansa ya kai ko’ina a lardunan, ikonsa ya yi ta ƙasaita gaba-gaba.
Förty Mardechai var myndig i Konungens hus, och hans rykte hördes i all land, huru han växte till, och vardt väldig.
5 Yahudawa suka karkashe dukan abokan gābansu da takobi, suka karkashe waɗanda suka ƙi jininsu, suka kuma hallaka su yadda suka ga dama.
Alltså slogo Judarna alla sina fiendar med svärd, dråpo och nederlade dem; och gjorde efter sin vilja på dem som dem fiender voro.
6 A mazaunin masarautar a Shusha, Yahudawa suka karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar.
Och i Susans stad slogo Judarna och dråpo femhundrad män.
7 Suka kuma kashe Farshandata, da Dalfon, da Asfata,
Dertill slogo de Parsandatha, Dalphon, Aspatha,
8 da Forata, da Adaliya, da Aridata,
Poratha, Adalja, Aridatha,
9 da Farmashta, da Arisai, da Aridai da kuma Baizata,
Parmastha, Arisai, Aridai, Vajesatha,
10 ’ya’ya maza goma na Haman ɗan Hammedata, abokin gāban Yahudawa. Amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
De tio Hamans söner, Medatha sons, Judarnas fiendas; men vid deras ägodelar kommo de intet.
11 A wannan rana, aka ba wa sarki rahoton yawan mutanen da aka kashe a mazaunin masarauta, a Shusha.
På samma tiden kom talet på de slagna i Susans stad inför Konungen.
12 Sarki ya ce wa Sarauniya Esta, “Yahudawa sun karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar, da kuma’ya’ya maza goma na Haman a mazaunin masarauta a Shusha. Me suka yi a sauran lardunan sarki? Yanzu kuma mene ne roƙonki? Za a ba ki. Mece ce bukatarki? Za a biya miki.”
Och Konungen sade till Drottningen Esther: Judarna hafva i Susans stad slagit och nederlagt femhundrad män, och de tio Hamans söner; hvad skola de göra i de andra Konungens land? Hvad bedes du, att man dig gifva skall? Och hvad begärar du mer, att man göra skall?
13 Esta ta ce, “In sarki ya yarda, yă ba wa Yahudawa da suke Shusha izini su aikata dokan nan gobe kuma, bari kuma a rataye’ya’ya maza goma na Haman a kan gumagumai.”
Esther sade: Om Konungenom täcktes, så låte han ock i morgon Judarna göra i Susan efter det bud, som i dag varit hafver, att de måga hänga de tio Hamans söner i galga.
14 Sai sarki ya ba da umarni a yi haka ɗin. Aka ba da doka a Shusha, aka kuma rataye’ya’ya maza goma na Haman.
Och Konungen befallde att göra så; och budet vardt i Susan uppslaget, och de tio Hamans söner vordo hängde.
15 Yahudawan da suke Shusha suka taru a ran goma sha huɗu na watan Adar suka kuma karkashe mutum ɗari uku a Shusha, amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
Och Judarna församlade sig i Susan på fjortonde dagen i den månaden Adar, och slogo ihjäl i Susan trehundrad män; men vid deras ägodelar kommo de intet.
16 Ana cikin haka, sai saura Yahudawa waɗanda suke lardunan sarki su ma suka taru domin su kāre kansu su kuma sami hutu daga abokan gābansu. Suka karkashe mutum dubu saba’in da biyar amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
Men de andre Judar i Konungens landom kommo tillsamman, och stodo för sitt lif, att de måtte göra sig rolighet för sina fiendar, och slogo sina fiendar fem och sjutio tusend; men vid deras ägodelar kommo de intet.
17 Wannan ya faru a ran goma sha uku na watan Adar. A rana ta goma sha huɗu kuwa suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da kuma ta farin ciki.
Detta skedde på trettonde dagen i den månaden Adar; och på fjortonde dagen i samma månadenom höllo de hvilo; den gjorde de sig till en vällusts och fröjds dag.
18 Amma Yahudawan da suke a Shusha suka taru a rana ta goma sha uku da ta sha huɗu, sa’an nan a rana ta goma sha biyar suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da ta farin ciki.
Men de Judar i Susan voro tillsammankomne, både på trettonde och fjortonde dagen, och höllo hvilo på femtonde dagen; och den dagen gjorde man till en vällusts och glädjes dag.
19 Shi ya sa Yahudawan ƙauyuka, waɗanda suke zama a karkara, suke kiyaye rana ta goma sha huɗu ta watan Adar a matsayin ranar farin ciki da ta biki, ranar ba da kyautai ga juna.
Derföre gjorde de Judar, som på bygdene och i småstäderna bodde, den fjortonde dagen i den månaden Adar till en vällusts och glädjes dag, och sände den ene dem andra skänker.
20 Sai Mordekai ya rubuta waɗannan abubuwa, ya kuma aika wasiƙu ga dukan Yahudawa ko’ina a lardunan Sarki Zerzes, na kusa da na nesa.
Och Mardechai skref allt detta som skedt var, och sände brefven till alla Judar, som voro uti all Konung Ahasveros land, både när och fjerran;
21 Ya sa su yi bikin kowace shekara a ranaku goma sha huɗu da goma sha biyar na watan Adar
Att de skulle vedertaga och hålla den fjortonde och femtonde dagen i den månadenom Adar, hvart år;
22 a matsayin lokacin da Yahudawa suka sami huta daga abokan gābansu, da kuma a matsayin watan da aka mai da baƙin cikinsu ya zama farin ciki, makokinsu kuma ya zama ranar biki. Ya rubuta musu su kiyaye ranakun a matsayin ranakun biki da na farin ciki. Su kuma ba da kyautai na abinci ga juna, da kuma kyautai ga matalauta.
Efter de dagar, i hvilka Judarna till ro komne voro för sina fiendar, och efter den månaden, i hvilkom deras sorg och glädje, och deras gråt i vällust vänd vardt; att de skulle dem hålla för vällusts och glädjes dagar, och sända den ene dem andra skänker, och dela med de fattiga.
23 Ta haka, Yahudawa suka yarda su ci gaba da bikin da suka fara, suna aikata abin da Mordekai ya rubuta musu.
Och Judarna togo dervid, och gjorde som de begynt hade, och det Mardechai till dem skref;
24 Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban dukan Yahudawa, ya ƙulla maƙarƙashiya game da Yahudawa, domin a hallaka su, ya kuma jefa fur (wato, ƙuri’a) don yă hallaka su.
Huruledes Haman, Medatha son, den Agagiten, alla Judars fiende, hade i sinnet att förgöra alla Judar, och låta kasta lott, till att förskräcka och förgöra dem;
25 Amma sa’ad da sarki ya sami labarin maƙarƙashiyar, sai ya ba da umarnai a rubuce cewa mugun shirin da Haman ya ƙulla a kan Yahudawa yă komo kansa, kuma cewa a rataye shi da’ya’yansa maza a kan gumagumai.
Och huru Esther hade ingångit till Konungen och beställt, att hans onda uppsåt, som han emot Judarna tänkte, måtte genom bref vändas inpå hans hufvud; och huru man honom och hans söner hade hängt i galga;
26 (Saboda haka, aka kira ranakun nan Furim, daga kalma fur). Saboda dukan abin da aka rubuta cikin wannan wasiƙa da kuma abin da suka gani, da abin da ya same su.
Af hvilko desse dagar kallades Purim, efter lottsnamnet, efter all detta brefs ord, och hvad de sjelfve sett hade, och hvad till dem räckt hade.
27 Yahudawa suka ɗauki nawayar kafa al’adar cewa su, da zuriyarsu, da dukan waɗanda suka haɗa hannun da su, za su kiyaye waɗannan kwanaki biyu, kowace shekara yadda aka tsara, a kuma lokacin da aka keɓe dominsu.
Och Judarna togo det uppå sig och sina säd, och uppå alla dem som gåfvo sig till dem, att de icke ville gå härifrå;
28 Za a tuna, a kuma kiyaye waɗannan kwanaki a kowane zamani, cikin kowane iyali, da kuma cikin kowane lardi, da kowace birni. Kuma kada Yahudawa su fasa yin bikin waɗannan kwanakin Furim, ko su bar jikokinsu su manta da kiyaye waɗannan ranaku biyu.
Att de ju ville hålla dessa två dagarna hvart år, såsom de föreskrefne och förelagde voro, så att desse dagar icke skulle förgätne, utan hållne varda, barn efter barn i alla slägter, i all land och städer; det äro de dagar Purim, hvilke icke skola brutne varda ibland Judarna, och deras åminnelse icke förgås när deras säd.
29 Saboda haka Sarauniya Esta,’yar Abihayil, tare da Mordekai mutumin Yahuda, suka rubuta da cikakken iko, suka tabbatar da wannan wasiƙa ta biyu game da Furim.
Och Drottningen Esther, Abihails dotter, och Mardechai den Juden, skrefvo med alla magt, till att fast göra detta andra brefvet om Purim;
30 Mordekai kuwa ya aika da wasiƙu zuwa ga dukan Yahudawa cikin larduna 127 na masarautar Zerzes. Saƙon fatan alheri da na tabbaci,
Och sände brefven till alla Judar, uti de hundrade sju och tjugu land i Konungs Ahasveros rike, med vänlig och trofast ord;
31 don a kafa waɗannan ranakun Furim a keɓaɓɓen lokacinsu, kamar yadda Mordekai mutumin Yahuda da Sarauniya Esta suka dokace su. Yadda kuma suka kafa wa kansu da zuriyarsu, game da lokutansu na azumi da makoki.
Att de skulle hålla dessa dagar Purim på deras bestämda tid, såsom Mardechai den Juden, och Drottningen Esther dem förelagt hade; såsom de uppå sina själar och uppå sina säd anammat hade det ärendet om fastone och ropet.
32 Dokar Esta ta tabbatar da waɗannan umarnai game da Furim, aka kuma rubuta ta cikin tarihi.
Och Esther befallde stadfästa detta ärendet om Purim, och skrifva uti en bok.