< Esta 9 >

1 A rana ta goma sha uku na watan goma sha biyu, wato, watan Adar ne za a aiwatar da dokar da sarki ya umarta. A wannan rana, abokan gāban Yahudawa suka sa zuciya za su sha ƙarfinsu, amma yanzu Zerzes ya canja, Yahudawa kuma suka yi galiba a bisa waɗanda suka ƙi jininsu.
و در روز سیزدهم ماه دوازدهم که ماه آذارباشد، هنگامی که نزدیک شد که حکم وفرمان پادشاه را جاری سازند و دشمنان یهودمنتظر می‌بودند که بر ایشان استیلا یابند، این همه برعکس شد که یهودیان بر دشمنان خویش استیلا یافتند.۱
2 Yahudawa suka tattaru a cikin biranensu a dukan lardunan Sarki Zerzes don su kai wa waɗanda suka nemi a hallaka su hari. Babu wanda ya tasar musu domin mutanen dukan sauran al’ummai sun jin tsoronsu.
و یهودیان در شهرهای خود درهمه ولایتهای اخشورش پادشاه جمع شدند تا برآنانی که قصد اذیت ایشان داشتند، دست بیندازندو کسی با ایشان مقاومت ننمود زیرا که ترس ایشان بر همه قومها مستولی شده بود.۲
3 Dukan sarakuna larduna, da hakimai, da gwamnoni da kuma ma’aikatan sarki suka taimaki Yahudawa, domin tsoron Mordekai ya kama su.
و جمیع روسای ولایتها و امیران و والیان و عاملان پادشاه، یهودیان را اعانت کردند زیرا که ترس مردخای برایشان مستولی شده بود،۳
4 Mordekai babban mutum ne a fada, sunansa ya kai ko’ina a lardunan, ikonsa ya yi ta ƙasaita gaba-gaba.
چونکه مردخای درخانه پادشاه معظم شده بود و آوازه او در جمیع ولایتها شایع گردیده و این مردخای آن فان بزرگتر می‌شد.۴
5 Yahudawa suka karkashe dukan abokan gābansu da takobi, suka karkashe waɗanda suka ƙi jininsu, suka kuma hallaka su yadda suka ga dama.
پس یهودیان جمیع دشمنان خود را به دم شمشیر زده، کشتند و هلاک کردند و با ایشان هرچه خواستند، به عمل آوردند.۵
6 A mazaunin masarautar a Shusha, Yahudawa suka karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar.
و یهودیان دردارالسلطنه شوشن پانصد نفر را به قتل رسانیده، هلاک کردند.۶
7 Suka kuma kashe Farshandata, da Dalfon, da Asfata,
و فرشنداطا و دلفون و اسفاتا،۷
8 da Forata, da Adaliya, da Aridata,
وفوراتا و ادلیا و اریداتا،۸
9 da Farmashta, da Arisai, da Aridai da kuma Baizata,
و فرمشتا و اریسای واریدای و یزاتا،۹
10 ’ya’ya maza goma na Haman ɗan Hammedata, abokin gāban Yahudawa. Amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
یعنی ده پسر هامان بن همداتای، دشمن یهود را کشتند، لیکن دست خود را به تاراج نگشادند.۱۰
11 A wannan rana, aka ba wa sarki rahoton yawan mutanen da aka kashe a mazaunin masarauta, a Shusha.
در آن روز، عدد آنانی را که در دارالسلطنه شوشن کشته شدند به حضور پادشاه عرضه داشتند.۱۱
12 Sarki ya ce wa Sarauniya Esta, “Yahudawa sun karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar, da kuma’ya’ya maza goma na Haman a mazaunin masarauta a Shusha. Me suka yi a sauran lardunan sarki? Yanzu kuma mene ne roƙonki? Za a ba ki. Mece ce bukatarki? Za a biya miki.”
و پادشاه به استر ملکه گفت که «یهودیان در دارالسلطنه شوشن پانصد نفر و ده پسر هامان را کشته و هلاک کرده‌اند. پس در سایرولایتهای پادشاه چه کرده‌اند؟ حال مسول توچیست که به تو داده خواهد شد و دیگر‌چه درخواست داری که برآورده خواهد گردید؟»۱۲
13 Esta ta ce, “In sarki ya yarda, yă ba wa Yahudawa da suke Shusha izini su aikata dokan nan gobe kuma, bari kuma a rataye’ya’ya maza goma na Haman a kan gumagumai.”
استر گفت: «اگر پادشاه را پسند آید به یهودیانی که در شوشن می‌باشند، اجازت داده شود که فردا نیز مثل فرمان امروز عمل نمایند وده پسر هامان را بردار بیاویزند.»۱۳
14 Sai sarki ya ba da umarni a yi haka ɗin. Aka ba da doka a Shusha, aka kuma rataye’ya’ya maza goma na Haman.
و پادشاه فرمود که چنین بشود و حکم در شوشن نافذگردید و ده پسر هامان را به دار آویختند.۱۴
15 Yahudawan da suke Shusha suka taru a ran goma sha huɗu na watan Adar suka kuma karkashe mutum ɗari uku a Shusha, amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
ویهودیانی که در شوشن بودند، در روز چهاردهم ماه آذار نیز جمع شده، سیصد نفر را در شوشن کشتند، لیکن دست خود را به تاراج نگشادند.۱۵
16 Ana cikin haka, sai saura Yahudawa waɗanda suke lardunan sarki su ma suka taru domin su kāre kansu su kuma sami hutu daga abokan gābansu. Suka karkashe mutum dubu saba’in da biyar amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
وسایر یهودیانی که در ولایتهای پادشاه بودندجمع شده، برای جانهای خود مقاومت نمودند وچون هفتاد و هفت هزار نفر از مبغضان خویش راکشته بودند، از دشمنان خود آرامی یافتند. امادست خود را به تاراج نگشادند.۱۶
17 Wannan ya faru a ran goma sha uku na watan Adar. A rana ta goma sha huɗu kuwa suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da kuma ta farin ciki.
این، در روز سیزدهم ماه آذار (واقع شد) ودر روز چهاردهم ماه، آرامی یافتند و آن را روزبزم و شادمانی نگاه داشتند.۱۷
18 Amma Yahudawan da suke a Shusha suka taru a rana ta goma sha uku da ta sha huɗu, sa’an nan a rana ta goma sha biyar suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da ta farin ciki.
و یهودیانی که در شوشن بودند، در سیزدهم و چهاردهم آن ماه جمع شدند و در روز پانزدهم ماه آرامی یافتند وآن را روز بزم و شادمانی نگاه داشتند.۱۸
19 Shi ya sa Yahudawan ƙauyuka, waɗanda suke zama a karkara, suke kiyaye rana ta goma sha huɗu ta watan Adar a matsayin ranar farin ciki da ta biki, ranar ba da kyautai ga juna.
بنابراین، یهودیان دهاتی که در دهات بی‌حصار ساکنند، روز چهاردهم ماه آذار را روز شادمانی و بزم وروز خوش نگاه می‌دارند و هدایا برای یکدیگرمی فرستند.۱۹
20 Sai Mordekai ya rubuta waɗannan abubuwa, ya kuma aika wasiƙu ga dukan Yahudawa ko’ina a lardunan Sarki Zerzes, na kusa da na nesa.
و مردخای این مطالب را نوشته، مکتوبات را نزد تمامی یهودیانی که در همه ولایتهای اخشورش پادشاه بودند، از نزدیک و دور فرستاد،۲۰
21 Ya sa su yi bikin kowace shekara a ranaku goma sha huɗu da goma sha biyar na watan Adar
تا بر ایشان فریضه‌ای بگذارد که روز چهاردهم و روز پانزدهم ماه آذار را سال به سال عید نگاه دارند.۲۱
22 a matsayin lokacin da Yahudawa suka sami huta daga abokan gābansu, da kuma a matsayin watan da aka mai da baƙin cikinsu ya zama farin ciki, makokinsu kuma ya zama ranar biki. Ya rubuta musu su kiyaye ranakun a matsayin ranakun biki da na farin ciki. Su kuma ba da kyautai na abinci ga juna, da kuma kyautai ga matalauta.
چونکه در آن روزها، یهودیان ازدشمنان خود آرامی یافتند و در آن ماه، غم ایشان به شادی و ماتم ایشان به روز خوش مبدل گردید. لهذا آنها را روزهای بزم و شادی نگاه بدارند وهدایا برای یکدیگر و بخششها برای فقیران بفرستند.۲۲
23 Ta haka, Yahudawa suka yarda su ci gaba da bikin da suka fara, suna aikata abin da Mordekai ya rubuta musu.
پس یهودیان آنچه را که خود به عمل نمودن آن شروع کرده بودند و آنچه را که مردخای به ایشان نوشته بود، بر خود فریضه ساختند.۲۳
24 Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban dukan Yahudawa, ya ƙulla maƙarƙashiya game da Yahudawa, domin a hallaka su, ya kuma jefa fur (wato, ƙuri’a) don yă hallaka su.
زیرا که هامان بن همداتای اجاجی، دشمن تمامی یهود، قصد هلاک نمودن یهودیان کرده و فور یعنی قرعه برای هلاکت و تلف نمودن ایشان انداخته بود.۲۴
25 Amma sa’ad da sarki ya sami labarin maƙarƙashiyar, sai ya ba da umarnai a rubuce cewa mugun shirin da Haman ya ƙulla a kan Yahudawa yă komo kansa, kuma cewa a rataye shi da’ya’yansa maza a kan gumagumai.
اما چون این امر به سمع پادشاه رسید، مکتوب حکم داد که قصد بدی که برای یهود اندیشیده بود، بر سر خودش برگردانیده شود و او را با پسرانش بر دار کشیدند.۲۵
26 (Saboda haka, aka kira ranakun nan Furim, daga kalma fur). Saboda dukan abin da aka rubuta cikin wannan wasiƙa da kuma abin da suka gani, da abin da ya same su.
از این جهت آن روزها را از اسم فور، فوریم نامیدند، و موافق تمامی مطلب این مکتوبات و آنچه خود ایشان در این امر دیده بودند و آنچه برایشان وارد آمده بود،۲۶
27 Yahudawa suka ɗauki nawayar kafa al’adar cewa su, da zuriyarsu, da dukan waɗanda suka haɗa hannun da su, za su kiyaye waɗannan kwanaki biyu, kowace shekara yadda aka tsara, a kuma lokacin da aka keɓe dominsu.
یهودیان این را فریضه ساختند و آن را بر ذمه خود و ذریت خویش وهمه کسانی که به ایشان ملصق شوند، گرفتند که تبدیل نشود و آن دو روز را برحسب کتابت آنها وزمان معین آنها سال به سال نگاه دارند.۲۷
28 Za a tuna, a kuma kiyaye waɗannan kwanaki a kowane zamani, cikin kowane iyali, da kuma cikin kowane lardi, da kowace birni. Kuma kada Yahudawa su fasa yin bikin waɗannan kwanakin Furim, ko su bar jikokinsu su manta da kiyaye waɗannan ranaku biyu.
و آن روزها را در همه طبقات و قبایل وولایتها و شهرها بیاد آورند و نگاه دارند و این‌روزهای فوریم، از میان یهود منسوخ نشود ویادگاری آنها از ذریت ایشان نابود نگردد.۲۸
29 Saboda haka Sarauniya Esta,’yar Abihayil, tare da Mordekai mutumin Yahuda, suka rubuta da cikakken iko, suka tabbatar da wannan wasiƙa ta biyu game da Furim.
واستر ملکه، دختر ابیحایل و مردخای یهودی، به اقتدار تمام نوشتند تا این مراسله دوم را درباره فوریم برقرار نمایند.۲۹
30 Mordekai kuwa ya aika da wasiƙu zuwa ga dukan Yahudawa cikin larduna 127 na masarautar Zerzes. Saƙon fatan alheri da na tabbaci,
و مکتوبات، مشتمل برسخنان سلامتی و امنیت نزد جمیع یهودیانی که در صد و بیست و هفت ولایت مملکت اخشورش بودند، فرستاد،۳۰
31 don a kafa waɗannan ranakun Furim a keɓaɓɓen lokacinsu, kamar yadda Mordekai mutumin Yahuda da Sarauniya Esta suka dokace su. Yadda kuma suka kafa wa kansu da zuriyarsu, game da lokutansu na azumi da makoki.
تا این دو روز فوریم را در زمان معین آنها فریضه قرار دهند، چنانکه مردخای یهودی و استر ملکه بر ایشان فریضه قرار دادند و ایشان آن را بر ذمه خود و ذریت خویش گرفتند، به یادگاری ایام روزه و تضرع ایشان.۳۱
32 Dokar Esta ta tabbatar da waɗannan umarnai game da Furim, aka kuma rubuta ta cikin tarihi.
پس سنن این فوریم، به فرمان استر فریضه شد و در کتاب مرقوم گردید.۳۲

< Esta 9 >