< Esta 9 >
1 A rana ta goma sha uku na watan goma sha biyu, wato, watan Adar ne za a aiwatar da dokar da sarki ya umarta. A wannan rana, abokan gāban Yahudawa suka sa zuciya za su sha ƙarfinsu, amma yanzu Zerzes ya canja, Yahudawa kuma suka yi galiba a bisa waɗanda suka ƙi jininsu.
Now in the twelfth month (that is the month of Adar), on the thirteenth day, when the king’s command and his decree was about to put into execution, on the day that the enemies of the Jews hoped to gain the mastery over them, then the tables were turned so that the Jews had the mastery over those who hated them.
2 Yahudawa suka tattaru a cikin biranensu a dukan lardunan Sarki Zerzes don su kai wa waɗanda suka nemi a hallaka su hari. Babu wanda ya tasar musu domin mutanen dukan sauran al’ummai sun jin tsoronsu.
The Jews gathered together in the cities throughout all the provinces of King Ahasuerus, to attack anyone who tried to harm them. No one could withstand them, for the fear of them had fallen on all the peoples.
3 Dukan sarakuna larduna, da hakimai, da gwamnoni da kuma ma’aikatan sarki suka taimaki Yahudawa, domin tsoron Mordekai ya kama su.
All the princes of the provinces and the satraps and the governors and they who attended to the king’s business, helped the Jews, because the fear of Mordecai had fallen on them.
4 Mordekai babban mutum ne a fada, sunansa ya kai ko’ina a lardunan, ikonsa ya yi ta ƙasaita gaba-gaba.
For Mordecai was great in the king’s palace, and as his power increased his fame spread throughout all the provinces.
5 Yahudawa suka karkashe dukan abokan gābansu da takobi, suka karkashe waɗanda suka ƙi jininsu, suka kuma hallaka su yadda suka ga dama.
The Jews put all their enemies to the sword and, with slaughter and destruction, they did what they wanted to those who hated them.
6 A mazaunin masarautar a Shusha, Yahudawa suka karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar.
In Susa the capital the Jews killed five hundred people.
7 Suka kuma kashe Farshandata, da Dalfon, da Asfata,
They killed Parshandatha, Dalphon, Aspatha,
8 da Forata, da Adaliya, da Aridata,
Poratha, Adalia, Aridatha,
9 da Farmashta, da Arisai, da Aridai da kuma Baizata,
Parmashta, Arisia, Aridai, and Vaizatha,
10 ’ya’ya maza goma na Haman ɗan Hammedata, abokin gāban Yahudawa. Amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
the ten sons of Haman the son of Hammedatha, the Jews’ enemy; but they did not take any plunder.
11 A wannan rana, aka ba wa sarki rahoton yawan mutanen da aka kashe a mazaunin masarauta, a Shusha.
On that day the number of those who were slain in Susa was brought before the king,
12 Sarki ya ce wa Sarauniya Esta, “Yahudawa sun karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar, da kuma’ya’ya maza goma na Haman a mazaunin masarauta a Shusha. Me suka yi a sauran lardunan sarki? Yanzu kuma mene ne roƙonki? Za a ba ki. Mece ce bukatarki? Za a biya miki.”
and the king said to Queen Esther, ‘The Jews have slain five hundred people in Susa, and the ten sons of Haman. What then have they done in the rest of the king’s provinces! Now what is your petition? It will be granted to you. What is your request? It will be done.’
13 Esta ta ce, “In sarki ya yarda, yă ba wa Yahudawa da suke Shusha izini su aikata dokan nan gobe kuma, bari kuma a rataye’ya’ya maza goma na Haman a kan gumagumai.”
‘If it please the king,’ Esther said, ‘let it be granted to the Jews who are in Susa to do tomorrow also according to this day’s decree. Let the bodies of Haman’s ten sons be hanged on the gallows.’
14 Sai sarki ya ba da umarni a yi haka ɗin. Aka ba da doka a Shusha, aka kuma rataye’ya’ya maza goma na Haman.
And the king commanded it to be done. A decree was given out in Susa and they hung the bodies of Haman’s ten sons on the gallows.
15 Yahudawan da suke Shusha suka taru a ran goma sha huɗu na watan Adar suka kuma karkashe mutum ɗari uku a Shusha, amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
The Jews who were in Susa gathered themselves together again on the fourteenth day of the month of Adar. They killed three hundred people in Susa. But they did not take any plunder.
16 Ana cikin haka, sai saura Yahudawa waɗanda suke lardunan sarki su ma suka taru domin su kāre kansu su kuma sami hutu daga abokan gābansu. Suka karkashe mutum dubu saba’in da biyar amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
And the other Jews who were in the king’s provinces gathered themselves together and fought for their lives and overcame their enemies. They killed seventy-five thousand who hated them. But they did not take any plunder.
17 Wannan ya faru a ran goma sha uku na watan Adar. A rana ta goma sha huɗu kuwa suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da kuma ta farin ciki.
This was on the thirteenth day of Adar. On the fourteenth day of the month Adar the Jews rested and made it a day of feasting and rejoicing.
18 Amma Yahudawan da suke a Shusha suka taru a rana ta goma sha uku da ta sha huɗu, sa’an nan a rana ta goma sha biyar suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da ta farin ciki.
(But the Jews in Susa gathered on both the thirteenth and fourteenth day – and rested on the fifteenth day of the same month and made it a day of feasting and rejoicing.)
19 Shi ya sa Yahudawan ƙauyuka, waɗanda suke zama a karkara, suke kiyaye rana ta goma sha huɗu ta watan Adar a matsayin ranar farin ciki da ta biki, ranar ba da kyautai ga juna.
This is why the Jews who live in the country villages keep the fourteenth day of the month of Adar as a day of rejoicing and feasting and a holiday, and a day in which they send gifts of food to each other.
20 Sai Mordekai ya rubuta waɗannan abubuwa, ya kuma aika wasiƙu ga dukan Yahudawa ko’ina a lardunan Sarki Zerzes, na kusa da na nesa.
Mordecai had these things recorded. He sent letters to all the Jews who were in all the provinces of the King Ahasuerus, both near and far.
21 Ya sa su yi bikin kowace shekara a ranaku goma sha huɗu da goma sha biyar na watan Adar
He told them to keep the fourteenth day of the month of Adar and also the fifteenth day every year,
22 a matsayin lokacin da Yahudawa suka sami huta daga abokan gābansu, da kuma a matsayin watan da aka mai da baƙin cikinsu ya zama farin ciki, makokinsu kuma ya zama ranar biki. Ya rubuta musu su kiyaye ranakun a matsayin ranakun biki da na farin ciki. Su kuma ba da kyautai na abinci ga juna, da kuma kyautai ga matalauta.
as the days on which the Jews had rest from their enemies, and the month which was turned from sorrow to gladness and from mourning into a feast day. They should make them days of feasting and gladness and of sending gifts of food to each other and of gifts to the poor.
23 Ta haka, Yahudawa suka yarda su ci gaba da bikin da suka fara, suna aikata abin da Mordekai ya rubuta musu.
So what the Jews had begun to do they adopted as a custom, just as Mordecai had written to them.
24 Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban dukan Yahudawa, ya ƙulla maƙarƙashiya game da Yahudawa, domin a hallaka su, ya kuma jefa fur (wato, ƙuri’a) don yă hallaka su.
For Haman the son of Hammedatha, the Agagite, the enemy of all the Jews, had plotted to destroy them. He had cast “Pur”, that is the lot, intending to consume them and to destroy them.
25 Amma sa’ad da sarki ya sami labarin maƙarƙashiyar, sai ya ba da umarnai a rubuce cewa mugun shirin da Haman ya ƙulla a kan Yahudawa yă komo kansa, kuma cewa a rataye shi da’ya’yansa maza a kan gumagumai.
But when the matter came before the king, he gave written orders that his wicked plot, which he had planned against the Jews, should come upon his own head, and that he and his sons should be hanged on the gallows.
26 (Saboda haka, aka kira ranakun nan Furim, daga kalma fur). Saboda dukan abin da aka rubuta cikin wannan wasiƙa da kuma abin da suka gani, da abin da ya same su.
This is why these days are called Purim, after the word Pur. Therefore because of all the words of this letter, as well as all they had seen, and all they had experienced,
27 Yahudawa suka ɗauki nawayar kafa al’adar cewa su, da zuriyarsu, da dukan waɗanda suka haɗa hannun da su, za su kiyaye waɗannan kwanaki biyu, kowace shekara yadda aka tsara, a kuma lokacin da aka keɓe dominsu.
the Jews established and made it a custom for them, for their descendants, and for all who should join them, so that it might not be repealed, that they should continue to observe these two days as feasts each year,
28 Za a tuna, a kuma kiyaye waɗannan kwanaki a kowane zamani, cikin kowane iyali, da kuma cikin kowane lardi, da kowace birni. Kuma kada Yahudawa su fasa yin bikin waɗannan kwanakin Furim, ko su bar jikokinsu su manta da kiyaye waɗannan ranaku biyu.
and that these days should be remembered and kept throughout every generation, every family, every province, and every city. And these days of Purim should not pass away from among the Jews nor the remembrance of them disappear among their descendants.
29 Saboda haka Sarauniya Esta,’yar Abihayil, tare da Mordekai mutumin Yahuda, suka rubuta da cikakken iko, suka tabbatar da wannan wasiƙa ta biyu game da Furim.
Queen Esther, the daughter of Abihail, gave Mordecai the Jew all authority in writing to confirm this second letter of Purim.
30 Mordekai kuwa ya aika da wasiƙu zuwa ga dukan Yahudawa cikin larduna 127 na masarautar Zerzes. Saƙon fatan alheri da na tabbaci,
He sent letters to all the Jews, to the hundred and twenty-seven provinces of the kingdom of Ahasuerus, wishing them peace and security,
31 don a kafa waɗannan ranakun Furim a keɓaɓɓen lokacinsu, kamar yadda Mordekai mutumin Yahuda da Sarauniya Esta suka dokace su. Yadda kuma suka kafa wa kansu da zuriyarsu, game da lokutansu na azumi da makoki.
to confirm these days of Purim in their proper times, to be observed as Mordecai the Jew and Queen Esther had directed and as the Jews had proscribed for themselves and their descendants, in the matter of the fastings and their cry of lamentation.
32 Dokar Esta ta tabbatar da waɗannan umarnai game da Furim, aka kuma rubuta ta cikin tarihi.
And the commands of Esther confirmed these matters of Purim; and it was written in the records.