< Esta 9 >

1 A rana ta goma sha uku na watan goma sha biyu, wato, watan Adar ne za a aiwatar da dokar da sarki ya umarta. A wannan rana, abokan gāban Yahudawa suka sa zuciya za su sha ƙarfinsu, amma yanzu Zerzes ya canja, Yahudawa kuma suka yi galiba a bisa waɗanda suka ƙi jininsu.
And in the twelfth month—it [is] the month of Adar—on the thirteenth day of it, in which the word of the king, even his law, has come to be done, in the day that the enemies of the Jews had hoped to rule over them, and it is turned that the Jews rule over those hating them—
2 Yahudawa suka tattaru a cikin biranensu a dukan lardunan Sarki Zerzes don su kai wa waɗanda suka nemi a hallaka su hari. Babu wanda ya tasar musu domin mutanen dukan sauran al’ummai sun jin tsoronsu.
the Jews have been assembled in their cities, in all provinces of King Ahasuerus, to put forth a hand on those seeking their evil, and no man has stood in their presence, for their fear has fallen on all the peoples.
3 Dukan sarakuna larduna, da hakimai, da gwamnoni da kuma ma’aikatan sarki suka taimaki Yahudawa, domin tsoron Mordekai ya kama su.
And all heads of the provinces, and the lieutenants, and the governors, and those doing the work that the king has, are lifting up the Jews, for a fear of Mordecai has fallen on them;
4 Mordekai babban mutum ne a fada, sunansa ya kai ko’ina a lardunan, ikonsa ya yi ta ƙasaita gaba-gaba.
for great [is] Mordecai in the house of the king, and his fame is going into all the provinces, for the man Mordecai is going on and becoming great.
5 Yahudawa suka karkashe dukan abokan gābansu da takobi, suka karkashe waɗanda suka ƙi jininsu, suka kuma hallaka su yadda suka ga dama.
And the Jews strike among all their enemies—a striking of the sword, and slaughter, and destruction—and do with those hating them according to their pleasure,
6 A mazaunin masarautar a Shusha, Yahudawa suka karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar.
and in Shushan the palace the Jews have slain and destroyed five hundred men;
7 Suka kuma kashe Farshandata, da Dalfon, da Asfata,
and Parshandatha, and Dalphon, and Aspatha,
8 da Forata, da Adaliya, da Aridata,
and Poratha, and Adalia, and Aridatha,
9 da Farmashta, da Arisai, da Aridai da kuma Baizata,
and Parmashta, and Arisai, and Aridai, and Vajezatha,
10 ’ya’ya maza goma na Haman ɗan Hammedata, abokin gāban Yahudawa. Amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
ten sons of Haman son of Hammedatha, adversary of the Jews, they have slain, and on the prey they have not put forth their hand.
11 A wannan rana, aka ba wa sarki rahoton yawan mutanen da aka kashe a mazaunin masarauta, a Shusha.
On that day has come the number of the slain in Shushan the palace before the king,
12 Sarki ya ce wa Sarauniya Esta, “Yahudawa sun karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar, da kuma’ya’ya maza goma na Haman a mazaunin masarauta a Shusha. Me suka yi a sauran lardunan sarki? Yanzu kuma mene ne roƙonki? Za a ba ki. Mece ce bukatarki? Za a biya miki.”
and the king says to Esther the queen, “In Shushan the palace the Jews have slain and destroyed five hundred men, and the ten sons of Haman; in the rest of the provinces of the king what have they done? And what [is] your petition? And it is given to you; and what your request again? And it is done.”
13 Esta ta ce, “In sarki ya yarda, yă ba wa Yahudawa da suke Shusha izini su aikata dokan nan gobe kuma, bari kuma a rataye’ya’ya maza goma na Haman a kan gumagumai.”
And Esther says, “If [it is] good to the king, let it also be given tomorrow, to the Jews who [are] in Shushan, to do according to the law of today; and the ten sons of Haman they hang on the tree.”
14 Sai sarki ya ba da umarni a yi haka ɗin. Aka ba da doka a Shusha, aka kuma rataye’ya’ya maza goma na Haman.
And the king commands [for it] to be done so; and a law is given in Shushan, and they have hanged the ten sons of Haman.
15 Yahudawan da suke Shusha suka taru a ran goma sha huɗu na watan Adar suka kuma karkashe mutum ɗari uku a Shusha, amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
And the Jews who [are] in Shushan are also assembled on the fourteenth day of the month of Adar, and they slay three hundred men in Shushan, and they have not put forth their hand on the prey.
16 Ana cikin haka, sai saura Yahudawa waɗanda suke lardunan sarki su ma suka taru domin su kāre kansu su kuma sami hutu daga abokan gābansu. Suka karkashe mutum dubu saba’in da biyar amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
And the rest of the Jews, who [are] in the provinces of the king, have been assembled, even to stand for their life, and to rest from their enemies, and to slay seventy-five thousand among those hating them, and they have not put forth their hand on the prey;
17 Wannan ya faru a ran goma sha uku na watan Adar. A rana ta goma sha huɗu kuwa suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da kuma ta farin ciki.
on the thirteenth day of the month of Adar, even to rest on the fourteenth of it, and to make it a day of banquet and of joy.
18 Amma Yahudawan da suke a Shusha suka taru a rana ta goma sha uku da ta sha huɗu, sa’an nan a rana ta goma sha biyar suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da ta farin ciki.
And the Jews who [are] in Shushan have been assembled, on the thirteenth day of it, and on the fourteenth of it, even to rest on the fifteenth of it, and to make it a day of banquet and of joy.
19 Shi ya sa Yahudawan ƙauyuka, waɗanda suke zama a karkara, suke kiyaye rana ta goma sha huɗu ta watan Adar a matsayin ranar farin ciki da ta biki, ranar ba da kyautai ga juna.
Therefore the Jews of the open places, who are dwelling in cities of the open places, are making the fourteenth day of the month of Adar—joy and banquet, and a good day, and of sending portions to one another.
20 Sai Mordekai ya rubuta waɗannan abubuwa, ya kuma aika wasiƙu ga dukan Yahudawa ko’ina a lardunan Sarki Zerzes, na kusa da na nesa.
And Mordecai writes these things, and sends letters to all the Jews who [are] in all provinces of King Ahasuerus, who are near and who are far off,
21 Ya sa su yi bikin kowace shekara a ranaku goma sha huɗu da goma sha biyar na watan Adar
to establish on them, to be keeping the fourteenth day of the month of Adar, and the fifteenth day of it, in every year and year,
22 a matsayin lokacin da Yahudawa suka sami huta daga abokan gābansu, da kuma a matsayin watan da aka mai da baƙin cikinsu ya zama farin ciki, makokinsu kuma ya zama ranar biki. Ya rubuta musu su kiyaye ranakun a matsayin ranakun biki da na farin ciki. Su kuma ba da kyautai na abinci ga juna, da kuma kyautai ga matalauta.
as days on which the Jews have rested from their enemies, and the month that has been turned to them from sorrow to joy, and from mourning to a good day, to make them days of banquet and of joy, and of sending portions to one another, and gifts to the needy.
23 Ta haka, Yahudawa suka yarda su ci gaba da bikin da suka fara, suna aikata abin da Mordekai ya rubuta musu.
And the Jews have received that which they had begun to do, and that which Mordecai has written to them,
24 Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban dukan Yahudawa, ya ƙulla maƙarƙashiya game da Yahudawa, domin a hallaka su, ya kuma jefa fur (wato, ƙuri’a) don yă hallaka su.
because Haman son of Hammedatha the Agagite, adversary of all the Jews, had devised concerning the Jews to destroy them, and had caused to fall Pur—that [is] the lot—to crush them and to destroy them;
25 Amma sa’ad da sarki ya sami labarin maƙarƙashiyar, sai ya ba da umarnai a rubuce cewa mugun shirin da Haman ya ƙulla a kan Yahudawa yă komo kansa, kuma cewa a rataye shi da’ya’yansa maza a kan gumagumai.
and in her coming in before the king, he commanded with the letter, “Let his evil scheme that he devised against the Jews return on his own head,” and they have hanged him and his sons on the tree,
26 (Saboda haka, aka kira ranakun nan Furim, daga kalma fur). Saboda dukan abin da aka rubuta cikin wannan wasiƙa da kuma abin da suka gani, da abin da ya same su.
therefore they have called these days Purim—by the name of the lot—therefore, because of all the words of this letter, and what they have seen concerning this, and what has come to them,
27 Yahudawa suka ɗauki nawayar kafa al’adar cewa su, da zuriyarsu, da dukan waɗanda suka haɗa hannun da su, za su kiyaye waɗannan kwanaki biyu, kowace shekara yadda aka tsara, a kuma lokacin da aka keɓe dominsu.
the Jews have established and received on them, and on their seed, and on all those joined to them, and it does not pass away, to be keeping these two days according to their writing, and according to their season, in every year and year;
28 Za a tuna, a kuma kiyaye waɗannan kwanaki a kowane zamani, cikin kowane iyali, da kuma cikin kowane lardi, da kowace birni. Kuma kada Yahudawa su fasa yin bikin waɗannan kwanakin Furim, ko su bar jikokinsu su manta da kiyaye waɗannan ranaku biyu.
and these days are remembered and kept in every generation and generation, family and family, province and province, and city and city, and these days of Purim do not pass away from the midst of the Jews, and their memorial is not ended from their seed.
29 Saboda haka Sarauniya Esta,’yar Abihayil, tare da Mordekai mutumin Yahuda, suka rubuta da cikakken iko, suka tabbatar da wannan wasiƙa ta biyu game da Furim.
And Esther the queen, daughter of Abihail, writes, and Mordecai the Jew, with all might, to establish this second letter of Purim,
30 Mordekai kuwa ya aika da wasiƙu zuwa ga dukan Yahudawa cikin larduna 127 na masarautar Zerzes. Saƙon fatan alheri da na tabbaci,
and he sends letters to all the Jews, to the one hundred twenty-seven provinces of the kingdom of Ahasuerus—words of peace and truth—
31 don a kafa waɗannan ranakun Furim a keɓaɓɓen lokacinsu, kamar yadda Mordekai mutumin Yahuda da Sarauniya Esta suka dokace su. Yadda kuma suka kafa wa kansu da zuriyarsu, game da lokutansu na azumi da makoki.
to establish these days of Purim, in their seasons, as Mordecai the Jew has established on them, and Esther the queen, and as they had established on themselves, and on their seed—matters of the fastings, and of their cry.
32 Dokar Esta ta tabbatar da waɗannan umarnai game da Furim, aka kuma rubuta ta cikin tarihi.
And a saying of Esther has established these matters of Purim, and it is written in the Scroll.

< Esta 9 >