< Esta 8 >

1 A wannan rana, Sarki Zerzes ya ba wa Esta mallakar Haman, abokin gāban Yahudawa. Mordekai kuma ya zo gaban sarki, gama Esta ta faɗa yadda ta haɗa dangi da shi.
On that day did king Ahasuerus give the house of Haman the Jews' oppressor to Esther the queen. And Mordecai came before the king; for Esther had told what he was to her.
2 Sarki ya cire zobensa na hatimi, wanda ya karɓo daga Haman ya ba Mordekai. Esta kuma ta naɗa shi a kan mallakar Haman.
And the king took off his ring, which he had taken from Haman, and gave it to Mordecai. And Esther set Mordecai over the house of Haman.
3 Esta ta sāke roƙon sarki, ta fāɗi a ƙafafunsa tana kuka. Ta roƙe shi yă kawo ƙarshen mugun shirin nan na Haman, mutumin Agag; wanda ya shirya a kan Yahudawa.
And Esther spoke yet again before the king, and fell down at his feet, and besought him with tears to put away the mischief of Haman the Agagite, and his device which he had devised against the Jews.
4 Sai sarki ya miƙa wa Esta sandan sarauta na zinariya, ta kuwa tashi ta tsaya a gabansa.
And the king held out the golden sceptre toward Esther. And Esther arose and stood before the king,
5 Ta ce, “In sarki ya yarda, in kuma na sami tagomashi daga gare shi, idan kuma ya gamshe shi yă yi abin da yake daidai, idan yana jin daɗina, bari a rubuta umarni a soke hukuncin saƙonin da Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, ya shirya ya kuma rubuta domin a hallaka Yahudawa a dukan lardunan sarki.
and said, If it please the king and if I have found grace before him, and the thing seem right to the king, and I be pleasing in his sight, let it be written to reverse the letters devised by Haman the son of Hammedatha the Agagite, which he wrote to destroy the Jews that are in all the king's provinces.
6 Gama yaya zan jure da ganin masifa ta faɗa a kan mutanena? Yaya zan jure in ga an hallaka iyalina?”
For how shall I endure to see the evil that shall befall my people? and how shall I endure to see the destruction of my kindred?
7 Sarki Zerzes ya amsa wa Esta da Mordekai mutumin Yahuda, “Domin Haman ya kai wa Yahudawa hari, na ba da mallakarsa ga Esta, an kuma rataye shi a wurin rataye mai laifi.
And king Ahasuerus said to queen Esther and to Mordecai the Jew, Behold, I have given Esther the house of Haman, and him they have hanged upon the gallows, because he stretched forth his hand against the Jews.
8 Yanzu ku rubuta wata doka, a sunan sarki, a madadin Yahudawa, yadda kuka ga ya fi kyau ku kuma hatimce ta da zoben hatimin sarki, gama babu takardar da aka rubuta da sunan sarki, aka kuma hatimce da zobensa da za a iya sokewa.”
Write ye then for the Jews as seems good to you, in the king's name, and seal [it] with the king's ring. For a writing that is written in the king's name, and sealed with the king's ring, cannot be reversed.
9 Nan da nan aka kira magatakardun fada, a ranar ashirin da uku ga watan uku, wato, watan Siban. Suka rubuta dukan umarnan Mordekai ga Yahudawa, da kuma ga shugabanni, da gwamnoni, da hakiman larduna 127 tun daga Indiya har zuwa Kush. Aka rubuta waɗannan umarnan a rubutun kowane lardi, da kuma cikin harshen kowane mutane. Aka kuma rubuta ga Yahudawa a rubutunsu da harshensu.
Then were the king's scribes called at that time, in the third month, that is, the month Sivan, on the three and twentieth [day] thereof; and it was written according to all that Mordecai commanded, to the Jews, and to the satraps, and the governors, and the princes of the provinces which are from India even to Ethiopia, a hundred and twenty-seven provinces, to every province according to the writing thereof, and to every people according to their language, and to the Jews according to their writing and according to their language.
10 Mordekai ya yi rubutu da sunan Sarki Zerzes, ya hatimce saƙonin da zoben hatimin sarki, ya kuma aika da su ta hannun masu’yan aika a kan dawakai, waɗanda sukan hau dawakai masu gudu sosai, da aka yi kiwonsu musamman saboda sarki.
And he wrote in the name of king Ahasuerus, and sealed [it] with the king's ring, and sent letters by couriers on horseback riding on coursers, horses of blood reared in the breeding studs:
11 Dokar sarki ta ba wa Yahudawa a kowace birni izini su taru, su kuma kāre kansu, domin su hallaka, su kashe, su kuma hallaka kowace ƙungiyar mayaƙa, na kowace ƙasa, ko lardi, da wataƙila za su kai musu, da matansu, da yaransu hari; su kuma washe mallakar abokan gābansu.
[stating] that the king granted the Jews that were in every city to gather themselves together, and to stand for their life, to destroy, to slay, and to cause to perish, all the power of the people and province that might assault them, [their] little ones and women, and to [take] the spoil of them for a prey,
12 Ranar da aka shirya domin Yahudawa su yi wannan a dukan lardunan Sarki Zerzes, ita ce ranar goma sha uku ga watan goma sha biyu, wato, watan Adar.
upon one day in all the provinces of king Ahasuerus, upon the thirteenth of the twelfth month, that is, the month Adar.
13 Za a ba da kofi na rubutacciyar dokar a matsayin ƙa’ida a kowane lardi, a kuma sanar wa mutanen kowace ƙasa, domin Yahudawa su zauna da shiri a ranar, domin su ɗau fansa a kan maƙiyansu.
That the decree might be given in every province, a copy of the writing was published to all the peoples, and that the Jews should be ready against that day to avenge themselves on their enemies.
14 ’Yan aikan, a kan dawakan fada, suka fita a guje, umarnin sarki yana iza su. Aka kuma ba da dokar a mazaunin masarauta wadda take Shusha.
The couriers mounted on coursers [and] horses of blood went out, being hastened and pressed on by the king's commandment. And the decree was given at Shushan the fortress.
15 Mordekai kuwa ya fita a gaban sarki da rigunan sarauta, masu ruwan shuɗi, da fari, da babban kambi na zinariya, da alkyabba ta lilin mai ruwan shunayya. Aka yi sowa don murna a birnin Shusha.
And Mordecai went out from the presence of the king in royal apparel of blue and white, and with a great crown of gold, and with a mantle of byssus and purple; and the city of Shushan shouted and was glad.
16 Ga Yahudawa kuwa, lokaci ne na murna da farin ciki, da jin daɗi da bangirma.
The Jews had light, and joy, and gladness, and honour.
17 A kowane lardi da kowace birni, ko’ina da dokar sarki ta kai, aka yi farin ciki a cikin Yahudawa, cike da bukukkuwa. Yawan mutane da waɗansu ƙasashe suka zama Yahudawa, don tsoron Yahudawa ya kama su.
And in every province, and in every city, wherever the king's commandment and his decree came, the Jews had joy and gladness, a feast and a good day. And many among the peoples of the land became Jews; for the fear of the Jews had fallen upon them.

< Esta 8 >