< Esta 4 >

1 Sa’ad da Mordekai ya sami labari game da dukan abin da aka yi, sai ya yayyage rigunansa, ya sanya tsummokin makoki, ya zuba toka a kā, ya kuma shiga ciki birni yana kuka mai zafi da ƙarfi.
Or, quand Mardochée eut appris tout ce qui avait été fait, il déchira ses vêtements, se couvrit d'un sac et de cendre, et il sortit par la ville, criant d'un cri grand et amer.
2 Amma ya kai bakin ƙofar sarki ne kawai, gama ba a yarda wani sanye da tsummokin makoki yă shiga cikin birni ba.
Et il vint jusque devant la porte du roi; car il n'était point permis d'entrer dans le palais du roi, étant vêtu d'un sac.
3 Aka yi makoki sosai da azumi, da kuka mai zafi a cikin Yahudawa a kowane lardin da aka kai doka da kuma umarnin sarki. Mutane da yawa suka kwanta a cikin tsummokin makoki da kuma toka.
Et dans chaque province, dans les lieux où la parole du roi et son ordonnance parvinrent, les Juifs furent en grand deuil, jeûnant, pleurant et se lamentant; et plusieurs se couchaient sur le sac et la cendre.
4 Sa’ad da bayi da bābānnin Esta suka zo suka faɗa mata game da Mordekai, sai ta damu ƙwarai. Ta aika masa da riguna domin yă sa a maimakon tsummokin makoki, amma ya ƙi.
Les servantes d'Esther et ses eunuques vinrent et lui rapportèrent cela; et la reine fut fort effrayée, et elle envoya des vêtements pour en revêtir Mardochée, et pour qu'il ôtât son sac de dessus lui; mais il ne les accepta point.
5 Sai Esta ta kira Hatak, ɗaya daga cikin bābānnin sarkin da aka ba shi aikin lura da ita, ta umarce shi yă yi tambaya me ke damun Mordekai da kuma me ya jawo haka.
Alors Esther appela Hathac, un des eunuques du roi, qu'il avait établi pour la servir; et elle lui donna ordre de savoir de Mardochée ce que c'était et pourquoi il en usait ainsi.
6 Saboda haka Hatak ya tafi wurin Mordekai a dandalin birni, a gaban ƙofar sarki.
Hathac sortit donc vers Mardochée, sur la place de la ville qui était devant la porte du roi.
7 Mordekai ya faɗa masa duk abin da ya faru da shi, haɗe da yawan kuɗin da Haman ya yi alkawari zai zuba a ma’ajin fada don a hallaka Yahudawa.
Et Mardochée lui déclara tout ce qui lui était arrivé, et la somme d'argent qu'Haman avait promis de payer au trésor du roi, au sujet des Juifs, afin qu'on les détruisît.
8 Ya kuma ba shi kofi na rubutaccen doka na kakkaɓe su, wanda aka wallafa a Shusha don yă nuna wa Esta, yă bayyana mata. Mordekai ya faɗa wa Hatak yă iza ta tă tafi gaban sarki domin tă yi roƙo don jinƙai, tă kuma roƙe shi saboda mutanenta.
Et il lui donna une copie de l'ordonnance écrite, qui avait été publiée à Suse, en vue de les exterminer, pour qu'il la montrât à Esther, l'informât de tout, et lui ordonnât d'entrer chez le roi, afin de lui demander grâce et de le prier pour sa nation.
9 Hatak ya koma ya ba wa Esta rahoton abin da Mordekai ya faɗa.
Hathac vint donc, et rapporta à Esther les paroles de Mardochée.
10 Sa’an nan Esta ta umarce Hatak yă ce wa Mordekai,
Et Esther dit à Hathac, et lui commanda de dire à Mardochée:
11 “Dukan hafsoshin sarki da mutanen lardunan sarki sun san cewa duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, mace ko namiji, ba tare da an kira shi ba, doka ɗaya ce take kan mutum, wato, kisa. Abu guda kawai da ya sha bamban shi ne sai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don yă rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.”
Tous les serviteurs du roi et le peuple des provinces du roi savent que c'est une loi, la même pour tous, que quiconque, homme ou femme, entre chez le roi, dans la cour intérieure, sans y être appelé, est mis à mort; il n'y a que celui à qui le roi tend le sceptre d'or, qui puisse vivre; et moi je n'ai point été appelée pour entrer chez le roi depuis trente jours.
12 Sa’ad da aka kai wa Mordekai rahoton maganan Esta,
On rapporta donc les paroles d'Esther à Mardochée.
13 sai ya mayar da wannan amsa wa Esta cewa, “Kada ki yi tsammani cewa don kina a cikin gidan sarki, ke kaɗai cikin dukan Yahudawa za ki tsira.
Et Mardochée dit qu'on fît à Esther cette réponse: Ne pense pas que tu échapperas seule d'entre tous les Juifs parce que tu es dans la maison du roi.
14 Gama in kin yi shiru a wannan lokaci, taimako da ceto zai zo daga wani wuri saboda Yahudawa, amma ke da gidanki za ku hallaka. Wa ya san ko saboda irin wannan lokaci ne kika sami wannan muƙami?”
Car, si tu te tais en ce temps-ci, les Juifs respireront et seront délivrés par quelque autre moyen; mais toi et la maison de ton père, vous périrez. Et qui sait si tu n'es point parvenue à la royauté pour un temps comme celui-ci?
15 Sai Esta ta aika da wannan amsa ga Mordekai cewa,
Alors Esther dit qu'on fît cette réponse à Mardochée:
16 “Ka tafi, ka tattara dukan Yahudawan da suke Shusha, ku yi azumi saboda ni. Kada ku ci ko ku sha, dare da rana har kwana uku. Ni kuwa da bayina za mu yi azumi yadda kuke yi. Idan aka yi haka, zan tafi wurin sarki, ko da yake wannan karya doka ce. Idan na hallaka, to, na hallaka.”
Va, assemble tous les Juifs qui se trouvent à Suse, et jeûnez pour moi; ne mangez ni ne buvez de trois jours, tant la nuit que le jour; et pour moi et mes servantes, nous jeûnerons de même; puis je m'en irai ainsi vers le roi, bien que ce soit contre la loi; et s'il arrive que je périsse, je périrai!
17 Saboda haka, Mordekai ya tafi, ya aikata dukan umarnan Esta.
Mardochée s'en alla donc, et fit tout ce qu'Esther lui avait commandé.

< Esta 4 >