< Esta 4 >

1 Sa’ad da Mordekai ya sami labari game da dukan abin da aka yi, sai ya yayyage rigunansa, ya sanya tsummokin makoki, ya zuba toka a kā, ya kuma shiga ciki birni yana kuka mai zafi da ƙarfi.
Or quand Mardochée eut appris tout ce qui avait été fait, il déchira ses vêtements, et se couvrit d'un sac et de cendre, et il sortit par la ville, criant d'un cri grand et amer.
2 Amma ya kai bakin ƙofar sarki ne kawai, gama ba a yarda wani sanye da tsummokin makoki yă shiga cikin birni ba.
Et il vint jusqu'au devant de la porte du Roi; (car il n'était point permis d'entrer dans la porte du Roi étant vêtu d'un sac).
3 Aka yi makoki sosai da azumi, da kuka mai zafi a cikin Yahudawa a kowane lardin da aka kai doka da kuma umarnin sarki. Mutane da yawa suka kwanta a cikin tsummokin makoki da kuma toka.
Et en chaque province, dans les lieux où la parole du Roi et son ordonnance parvint, les Juifs furent en grand deuil, jeûnant, pleurant, et se lamentant; et plusieurs se couchaient sur le sac, et sur la cendre.
4 Sa’ad da bayi da bābānnin Esta suka zo suka faɗa mata game da Mordekai, sai ta damu ƙwarai. Ta aika masa da riguna domin yă sa a maimakon tsummokin makoki, amma ya ƙi.
Or les demoiselles d'Esther, et ses Eunuques vinrent et lui rapportèrent ces choses, et la Reine fut fort affligée, et elle envoya des vêtements pour en vêtir Mardochée, et afin qu'il ôtât son sac de dessus lui; mais il ne [les] prit point.
5 Sai Esta ta kira Hatak, ɗaya daga cikin bābānnin sarkin da aka ba shi aikin lura da ita, ta umarce shi yă yi tambaya me ke damun Mordekai da kuma me ya jawo haka.
Alors Esther appela Hatach l'un des Eunuques du Roi, lequel il avait établi pour la servir, et elle lui donna charge de savoir de Mardochée, ce que c'était, et pourquoi il en usait ainsi.
6 Saboda haka Hatak ya tafi wurin Mordekai a dandalin birni, a gaban ƙofar sarki.
Hatach donc sortit vers Mardochée en la place de la ville, qui était au devant de la porte du Roi.
7 Mordekai ya faɗa masa duk abin da ya faru da shi, haɗe da yawan kuɗin da Haman ya yi alkawari zai zuba a ma’ajin fada don a hallaka Yahudawa.
Et Mardochée lui déclara tout ce qui lui était arrivé, et l'offre de l'argent comptant qu'Haman avait promis de délivrer au trésor du Roi, à cause des Juifs, afin qu'on les détruisît.
8 Ya kuma ba shi kofi na rubutaccen doka na kakkaɓe su, wanda aka wallafa a Shusha don yă nuna wa Esta, yă bayyana mata. Mordekai ya faɗa wa Hatak yă iza ta tă tafi gaban sarki domin tă yi roƙo don jinƙai, tă kuma roƙe shi saboda mutanenta.
Et il lui donna une copie de l'ordonnance qui avait été mise par écrit, et qui avait été publiée dans Susan, afin de les exterminer, pour [la] montrer à Esther, et lui faire entendre le tout, et lui recommander d'entrer chez le Roi pour lui demander grâce, et lui faire requête pour sa nation.
9 Hatak ya koma ya ba wa Esta rahoton abin da Mordekai ya faɗa.
Ainsi Hatach revint, et rapporta à Esther les paroles de Mardochée.
10 Sa’an nan Esta ta umarce Hatak yă ce wa Mordekai,
Et Esther dit à Hatach, et lui commanda de dire à Mardochée:
11 “Dukan hafsoshin sarki da mutanen lardunan sarki sun san cewa duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, mace ko namiji, ba tare da an kira shi ba, doka ɗaya ce take kan mutum, wato, kisa. Abu guda kawai da ya sha bamban shi ne sai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don yă rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.”
Tous les serviteurs du Roi, et le peuple des provinces du Roi savent qu'il n'y a ni homme, ni femme qui entre chez le Roi au parvis de dedans, sans y être appelé, [et] que c'est une de ses lois, de le faire mourir; à moins que le Roi ne lui ait tendu le sceptre d'or, car en ce cas-là il a la vie sauve; or il y a déjà trente jours que je n'ai point été appelée pour entrer chez le Roi.
12 Sa’ad da aka kai wa Mordekai rahoton maganan Esta,
On rapporta donc les paroles d'Esther à Mardochée.
13 sai ya mayar da wannan amsa wa Esta cewa, “Kada ki yi tsammani cewa don kina a cikin gidan sarki, ke kaɗai cikin dukan Yahudawa za ki tsira.
Et Mardochée dit qu'on fit cette réponse à Esther: Ne pense pas en toi-même que [toi seule] d'entre tous les Juifs échappes dans la maison du Roi.
14 Gama in kin yi shiru a wannan lokaci, taimako da ceto zai zo daga wani wuri saboda Yahudawa, amma ke da gidanki za ku hallaka. Wa ya san ko saboda irin wannan lokaci ne kika sami wannan muƙami?”
Mais si tu te tais entièrement en ce temps-ci, les Juifs respireront et seront délivrés par quelque autre moyen; mais vous périrez, toi et la maison de ton père. Et qui sait si tu n'es point parvenue au Royaume pour un temps comme celui-ci?
15 Sai Esta ta aika da wannan amsa ga Mordekai cewa,
Alors Esther dit qu'on fit cette réponse à Mardochée:
16 “Ka tafi, ka tattara dukan Yahudawan da suke Shusha, ku yi azumi saboda ni. Kada ku ci ko ku sha, dare da rana har kwana uku. Ni kuwa da bayina za mu yi azumi yadda kuke yi. Idan aka yi haka, zan tafi wurin sarki, ko da yake wannan karya doka ce. Idan na hallaka, to, na hallaka.”
Va, assemble tous les Juifs qui se trouveront à Susan, et jeûnez pour moi, et ne mangez et ne buvez de trois jours, tant la nuit que le jour; et moi et mes demoiselles nous jeûnerons de même; puis je m'en irai ainsi vers le Roi, ce qui n'est point selon la Loi; et s'il arrive que je périsse, que je périsse.
17 Saboda haka, Mordekai ya tafi, ya aikata dukan umarnan Esta.
Mardochée donc s'en alla, et fit comme Esther lui avait commandé.

< Esta 4 >