< Esta 4 >
1 Sa’ad da Mordekai ya sami labari game da dukan abin da aka yi, sai ya yayyage rigunansa, ya sanya tsummokin makoki, ya zuba toka a kā, ya kuma shiga ciki birni yana kuka mai zafi da ƙarfi.
When Mordecai learned of all that had been done, he tore his clothes and put on sackcloth and ashes. He went out into the middle of the city, and cried out with a loud and a bitter cry.
2 Amma ya kai bakin ƙofar sarki ne kawai, gama ba a yarda wani sanye da tsummokin makoki yă shiga cikin birni ba.
He went up only as far as the king's gate, because no one was allowed to go through it clothed in sackcloth.
3 Aka yi makoki sosai da azumi, da kuka mai zafi a cikin Yahudawa a kowane lardin da aka kai doka da kuma umarnin sarki. Mutane da yawa suka kwanta a cikin tsummokin makoki da kuma toka.
In every province, wherever the king's command and decree reached, there was great mourning among the Jews, with fasting, weeping, and lamenting. Many of them lay in sackcloth and ashes.
4 Sa’ad da bayi da bābānnin Esta suka zo suka faɗa mata game da Mordekai, sai ta damu ƙwarai. Ta aika masa da riguna domin yă sa a maimakon tsummokin makoki, amma ya ƙi.
When Esther's young women and her servants came and told her, the queen was in great distress. She sent garments to clothe Mordecai (so he could take off his sackcloth), but he would not accept them.
5 Sai Esta ta kira Hatak, ɗaya daga cikin bābānnin sarkin da aka ba shi aikin lura da ita, ta umarce shi yă yi tambaya me ke damun Mordekai da kuma me ya jawo haka.
Then Esther called for Hathak, one of the king's officials who had been assigned to serve her. She ordered him to go to Mordecai to learn what had happened and what it meant.
6 Saboda haka Hatak ya tafi wurin Mordekai a dandalin birni, a gaban ƙofar sarki.
So Hathak went to Mordecai in the city square in front of the king's gate.
7 Mordekai ya faɗa masa duk abin da ya faru da shi, haɗe da yawan kuɗin da Haman ya yi alkawari zai zuba a ma’ajin fada don a hallaka Yahudawa.
Mordecai reported to him all that had happened to him, and the total amount of the silver that Haman had promised to weigh out and put into the king's treasuries in order to put the Jews to death.
8 Ya kuma ba shi kofi na rubutaccen doka na kakkaɓe su, wanda aka wallafa a Shusha don yă nuna wa Esta, yă bayyana mata. Mordekai ya faɗa wa Hatak yă iza ta tă tafi gaban sarki domin tă yi roƙo don jinƙai, tă kuma roƙe shi saboda mutanenta.
He also gave him a copy of the decree that was issued in Susa for the Jews' destruction. He did this so that Hathak could show it to Esther, and that he should give her the responsibility of going to the king to beg for his favor, and to plead with him on behalf of her people.
9 Hatak ya koma ya ba wa Esta rahoton abin da Mordekai ya faɗa.
So Hathak went and told Esther what Mordecai had said.
10 Sa’an nan Esta ta umarce Hatak yă ce wa Mordekai,
Then Esther spoke to Hathak and told him to go back to Mordecai.
11 “Dukan hafsoshin sarki da mutanen lardunan sarki sun san cewa duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, mace ko namiji, ba tare da an kira shi ba, doka ɗaya ce take kan mutum, wato, kisa. Abu guda kawai da ya sha bamban shi ne sai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don yă rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.”
She said, “All the king's servants and the people of the king's provinces know that if any man or woman goes to the king inside the inner courtyard without being summoned, there is only one law: That he must be put to death—except for anyone to whom the king holds out the golden scepter so that he may live. I have not been called to come to the king these thirty days.”
12 Sa’ad da aka kai wa Mordekai rahoton maganan Esta,
So Hathak reported Esther's words to Mordecai.
13 sai ya mayar da wannan amsa wa Esta cewa, “Kada ki yi tsammani cewa don kina a cikin gidan sarki, ke kaɗai cikin dukan Yahudawa za ki tsira.
Mordecai sent back this message: “You must not think that in the king's palace, you will escape any more than all the other Jews.
14 Gama in kin yi shiru a wannan lokaci, taimako da ceto zai zo daga wani wuri saboda Yahudawa, amma ke da gidanki za ku hallaka. Wa ya san ko saboda irin wannan lokaci ne kika sami wannan muƙami?”
If you remain silent at this time, relief and rescue will rise up for the Jews from another place, but you and your father's house will perish. Who knows whether you have come to this royal position for such a time as this?”
15 Sai Esta ta aika da wannan amsa ga Mordekai cewa,
Then Esther sent this message to Mordecai,
16 “Ka tafi, ka tattara dukan Yahudawan da suke Shusha, ku yi azumi saboda ni. Kada ku ci ko ku sha, dare da rana har kwana uku. Ni kuwa da bayina za mu yi azumi yadda kuke yi. Idan aka yi haka, zan tafi wurin sarki, ko da yake wannan karya doka ce. Idan na hallaka, to, na hallaka.”
“Go, gather together all the Jews who live in Susa, and fast for me. Do not eat nor drink for three days, night or day. My young girls and I will fast in the same way. Then I will go to the king, even though it is against the law, and if I perish, I perish.”
17 Saboda haka, Mordekai ya tafi, ya aikata dukan umarnan Esta.
Mordecai went and did all that Esther told him to do.