< Esta 2 >

1 Daga baya sa’ad da fushin Sarki Zerzes ya huce, sai ya tuna da Bashti da abin da ta yi, da kuma dokar da ya bayar game da ita.
After a while, King Xerxes quit being so angry. He thought about Vashti, and he thought about the law he had made because of what she [had done, and he wanted another wife].
2 Sai masu hidimar sarki na musamman, suka kawo shawara cewa, “Bari a nemi, kyawawan budurwai saboda sarki.
So his personal servants said to him, “[Your majesty, ] you should send some men to search throughout the empire for some beautiful young women/virgins for you.
3 Bari sarki yă naɗa komishinoni a kowane yanki na masarautarsa, domin su kawo dukan waɗannan kyawawan’yan mata cikin harabar mazaunin masarautar a Shusha. Bari a sa su a hannun Hegai, bābān sarki, wanda yake lura da mata, bari kuma a yi musu kulawa ta musamman.
[After they find some, ] you can appoint some officials in each province to bring them to the place where you keep (your wives/the women you sleep with) here in Susa. Then Hegai, the man who is in charge of these women, can arrange for ointments to be put [on their bodies] to make them [more] beautiful.
4 Sa’an nan bari yarinyar da ta gamshi sarki, tă zama sarauniya a maimakon Bashti.” Wannan shawara ta gamshi sarki, ya kuwa yi na’am da ita.
Then the woman who pleases you most can become queen instead of Vashti.” The king liked what they suggested, so he did it.
5 To, a cikin mazaunin masarauta a Shusha, akwai wani mutumin Yahuda, daga Kabilar Benyamin mai suna Mordekai, ɗan Yayir, ɗan Shimeyi, ɗan Kish,
At that time there was a Jew [living] in Susa, the capital, whose name was Mordecai, the son of Jair. Jair was a descendant of Shimei. Shimei was a descendant of [King Saul’s father] Kish. [They were all] from the tribe descended from Benjamin.
6 wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ɗauka tare’yan zaman bauta cikin waɗanda ya ɗauko daga Urushalima, tare da Yekoniya, sarkin Yahuda.
[Many years before that, ] King Nebuchadnezzar had taken (Mordecai/Mordecai’s family) [and brought them from Jerusalem] to Babylon, at the same time he brought King Jehoiachin of Judah and many other people to Babylon.
7 Mordekai yana da wata’yar kawunsa mai suna Hadassa, wanda ya yi reno, ba ta da mahaifi ko mahaifiya. Ita ce yarinyar da aka santa da suna Esta. Kyakkyawa ce ƙwarai. Mordekai dai ya ɗauke ta tamƙar’yarsa sa’ad da mahaifinta da mahaifiyarta suka mutu.
Mordecai had a cousin whose [Hebrew] name was Hadassah. She had a beautiful face and beautiful body/figure. Her [Persian] name was Esther. After her father and mother died, Mordecai took care of Esther as though she were his own daughter.
8 Da aka yi shelar umarni da dokar sarki, sai aka kawo’yan mata masu yawa a mazaunin masarauta a Shusha, aka kuma sa su ƙarƙashin kulawar Hegai. Aka kawo Esta ma zuwa fadar sarki, aka danƙa ta wa Hegai, wanda yake lura da mata.
After the king commanded [that they search for some beautiful women], they brought Esther and many other young women to the king’s palace [in Susa], and (the king put Hegai/Hegai was put) in charge of them.
9 Yarinyar ta gamshe shi, ta kuma sami tagomashinsa. Nan da nan ya tanada mata, ya ba ta man shafawa da abinci na musamman. Ya ba ta bayi mata bakwai da aka zaɓa daga fadar sarki. Ya kuma kai ta tare da bayinta zuwa wuri mafi kyau na gidan matan kulle.
Hegai was very pleased with Esther, and he treated her well. He immediately arranged for her to be given ointments to make her [even more] beautiful, and [he ordered that] special food [would be given to her]. [He arranged that] seven maids from the king’s palace [would take care of her], and arranged that she/they would stay in the best rooms.
10 Esta ba tă bayyana asalin al’ummarta da na iyalinta ba, domin Mordekai ya hana yin haka.
Esther did not tell anyone that she was a Jew, because Mordecai had told her not to tell anyone.
11 Kowace rana Mordekai yana kai da komowa kusa da harabar filin gidan matan kulle, domin ya san yadda Esta take, da kuma abin da yake faruwa da ita.
Every day Mordecai walked near the courtyard of the place where those women stayed. He asked [people who entered the courtyard] to find out [and tell him] what was happening to Esther.
12 Kafin a kai kowace yarinya wurin Sarki Zerzes, sai ta gama watanni goma sha biyu cif ana yin mata kwalliyar da aka tsara, akan ɗauki watanni shida ana shafa mata man mur, a ɗauki watanni shida kuma ana shafa mata man ƙanshi da kayan shafe-shafe.
Before these women were taken to the king, they put ointments on [the bodies of] these women for one year to make them more beautiful. For six months they [rubbed olive] oil mixed with myrrh [on their bodies each day]. For [the next] six months they rubbed ointments and perfumes on their bodies.
13 A kuma koya mata yadda za tă tafi wurin sarki. Aka ba ta duk abin da take so ta riƙe daga gidan matan kulle zuwa fadar sarki.
Then, when one of these women [was summoned to] go to the king, she was allowed to wear whatever clothes and jewelry she chose.
14 Da yamma za tă tafi can, da safe kuma ta dawo wani ɓangaren gidan matan kullen da yake a ƙarƙashin kulawar Sha’ashgaz, bābā na sarki, wanda yake lura da ƙwarƙwarai. Ba ta dawowa wurin sarki sai in ta gamshe shi, sai ya kuma kira ta da suna.
In the evening, they would take her [to the king’s own room]. The next morning, they would take her to another place where the women [who had slept with the king] stayed. There another official whose name was Shaashgaz was in charge [of those women]. [Those women would live there for the rest of their lives, and] one of those women would go back to the king again only if the king very much wanted her to come again, and only if he told Shaashgaz the name of the woman.
15 Sa’ad da lokaci ya yi da Esta (yarinyar da Mordekai ya ɗauka tamƙar’yarsa,’yar kawunsa Abihayil) za tă shiga wurin sarki, ba tă nemi a ba ta kome ba in ban da abin da Hegai, bābān sarki mai lura da gidan matan kulle, ya ba da shawara. Esta kuwa ta sami tagomashin kowa da ya ganta.
Everyone who saw Esther liked her. After King Xerxes had been ruling for seven years, it was Esther’s turn to go to him. When they took her to the king, it was during the middle part of the winter. She wore only the things that Hegai suggested.
16 Aka kai Esta wurin Sarki Zerzes a mazaunin sarauta a wata na goma, watan Tebet, a shekara ta bakwai ta mulkinsa.
17 To, sarki ya so Esta fiye da duk sauran matan, ta kuma sami tagomashinsa da kuma yardarsa fiye da duk sauran budurwai. Saboda haka ya sa rawanin sarauta a kanta, ya kuma mai da ita sarauniya a maimakon Bashti.
The king liked Esther more than he liked any of the other women [that they brought to him]. He liked her so much that he put on her head the queen’s crown, and he declared that Esther would be the queen instead of Vashti.
18 Sarki kuwa ya yi ƙasaitacciyar liyafa, liyafar Esta, wa dukan hakimansa da shugabannin masarautarsa. Ya yi shelar hutu ko’ina a larduna, ya kuma raba kyautai a yalwace irin na sarauta.
To celebrate her [becoming the queen], he had a big banquet/feast prepared for all his administrators and [other] officials. He generously gave [expensive] gifts to everyone, and he declared that in all the provinces there would be a holiday, [a time when people did not have to pay taxes].
19 Sa’ad da aka tara budurwai karo na biyu, Mordekai kuwa yana zama a bakin ƙofar sarki.
Later all those women who had spent a night with the king were gathered together again. By that time Mordecai had become an official at the palace.
20 Amma Esta ta ɓoye asalin iyalinta da na al’ummarta yadda Mordekai ya ce ta yi, gama ta ci gaba da bin umarnan Mordekai yadda take yi sa’ad da yake renonta.
But Esther still did not tell anyone that she was a Jew. She continued to do what Mordecai had told her to do.
21 Sa’ad da Mordekai yake zaune a bakin ƙofar sarki, sai Bigtana da Teresh, biyu daga cikin hafsoshin sarki masu gadin ƙofar shiga, suka yi fushi, suka kuma ƙulla su kashe sarki Zerzes.
One day when Mordecai was doing his work in the palace, two of the king’s officials were there. Their names were Bigthana and Teresh. They were the guards who stood outside the king’s own rooms. They became angry [with the king], and they were planning how they could assassinate/kill him.
22 Mordekai kuwa ya sami labarin makircin, ya kuma faɗa wa Sarauniya Esta, wadda ta faɗa wa sarki, ta kuma nuna masa cewa Mordekai ne ya ji.
But Mordecai heard about what they were planning, and he told that to Queen Esther. Then she told the king what Mordecai had found out.
23 Sa’ad da aka bincika labarin aka kuma iske gaskiya ne, sai aka rataye hafsoshin nan biyu a wurin rataye mai laifi. Aka rubuta dukan wannan a cikin littafin tarihi a gaban sarki.
The king investigated and found out that Mordecai’s report was true. So the king ordered that those two men be hanged. When that was done, (an official wrote a report/a report was written) about it in a book called ‘The book that records what happened while Xerxes was king’.

< Esta 2 >