< Esta 2 >
1 Daga baya sa’ad da fushin Sarki Zerzes ya huce, sai ya tuna da Bashti da abin da ta yi, da kuma dokar da ya bayar game da ita.
After these things, at the ceasing of the fury of King Ahasuerus, he has remembered Vashti, and that which she did, and that which has been decreed concerning her;
2 Sai masu hidimar sarki na musamman, suka kawo shawara cewa, “Bari a nemi, kyawawan budurwai saboda sarki.
and servants of the king, his ministers, say, “Let them seek for the king young women, virgins, of good appearance,
3 Bari sarki yă naɗa komishinoni a kowane yanki na masarautarsa, domin su kawo dukan waɗannan kyawawan’yan mata cikin harabar mazaunin masarautar a Shusha. Bari a sa su a hannun Hegai, bābān sarki, wanda yake lura da mata, bari kuma a yi musu kulawa ta musamman.
and the king appoints inspectors in all provinces of his kingdom, and they gather every young woman—virgin, of good appearance—to Shushan the palace, to the house of the women, to the hand of Hegai eunuch of the king, keeper of the women, and to give their purifications,
4 Sa’an nan bari yarinyar da ta gamshi sarki, tă zama sarauniya a maimakon Bashti.” Wannan shawara ta gamshi sarki, ya kuwa yi na’am da ita.
and the young woman who is good in the eyes of the king reigns instead of Vashti”; and the thing is good in the eyes of the king, and he does so.
5 To, a cikin mazaunin masarauta a Shusha, akwai wani mutumin Yahuda, daga Kabilar Benyamin mai suna Mordekai, ɗan Yayir, ɗan Shimeyi, ɗan Kish,
A man, a Jew, there has been in Shushan the palace, and his name [is] Mordecai son of Jair, son of Shimei, son of Kish, a Benjamite—
6 wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ɗauka tare’yan zaman bauta cikin waɗanda ya ɗauko daga Urushalima, tare da Yekoniya, sarkin Yahuda.
who had been removed from Jerusalem with the expulsion that was removed with Jeconiah king of Judah, whom Nebuchadnezzar king of Babylon removed—
7 Mordekai yana da wata’yar kawunsa mai suna Hadassa, wanda ya yi reno, ba ta da mahaifi ko mahaifiya. Ita ce yarinyar da aka santa da suna Esta. Kyakkyawa ce ƙwarai. Mordekai dai ya ɗauke ta tamƙar’yarsa sa’ad da mahaifinta da mahaifiyarta suka mutu.
and he is supporting Hadassah—she [is] Esther—daughter of his uncle, for she has neither father nor mother, and the young woman [is] of beautiful form, and of good appearance, and at the death of her father and her mother Mordecai has taken her to himself for a daughter.
8 Da aka yi shelar umarni da dokar sarki, sai aka kawo’yan mata masu yawa a mazaunin masarauta a Shusha, aka kuma sa su ƙarƙashin kulawar Hegai. Aka kawo Esta ma zuwa fadar sarki, aka danƙa ta wa Hegai, wanda yake lura da mata.
And it comes to pass, in the word of the king, even his law, being heard, and in many young women being gathered to Shushan the palace, to the hand of Hegai, that Esther is taken to the house of the king, to the hand of Hegai, keeper of the women,
9 Yarinyar ta gamshe shi, ta kuma sami tagomashinsa. Nan da nan ya tanada mata, ya ba ta man shafawa da abinci na musamman. Ya ba ta bayi mata bakwai da aka zaɓa daga fadar sarki. Ya kuma kai ta tare da bayinta zuwa wuri mafi kyau na gidan matan kulle.
and the young woman is good in his eyes, and she receives kindness before him, and he hurries her purifications and her portions—to give to her, and the seven young women who are provided—to give to her, from the house of the king, and he changes her and her young women to a good [place in] the house of the women.
10 Esta ba tă bayyana asalin al’ummarta da na iyalinta ba, domin Mordekai ya hana yin haka.
Esther has not declared her people, and her family, for Mordecai has laid a charge on her that she does not declare [it];
11 Kowace rana Mordekai yana kai da komowa kusa da harabar filin gidan matan kulle, domin ya san yadda Esta take, da kuma abin da yake faruwa da ita.
and during every day Mordecai is walking up and down before the court of the house of the women to know the welfare of Esther, and what is done with her.
12 Kafin a kai kowace yarinya wurin Sarki Zerzes, sai ta gama watanni goma sha biyu cif ana yin mata kwalliyar da aka tsara, akan ɗauki watanni shida ana shafa mata man mur, a ɗauki watanni shida kuma ana shafa mata man ƙanshi da kayan shafe-shafe.
And in the drawing near of the turn of each young woman to come in to King Ahasuerus, at the end of there being to her—according to the law of the women—twelve months, for so they fulfill the days of their purifications; six months with oil of myrrh, and six months with perfumes, and with the purifications of women,
13 A kuma koya mata yadda za tă tafi wurin sarki. Aka ba ta duk abin da take so ta riƙe daga gidan matan kulle zuwa fadar sarki.
and with this the young woman has come in to the king, all that she says is given to her to go in with her out of the house of the women to the house of the king;
14 Da yamma za tă tafi can, da safe kuma ta dawo wani ɓangaren gidan matan kullen da yake a ƙarƙashin kulawar Sha’ashgaz, bābā na sarki, wanda yake lura da ƙwarƙwarai. Ba ta dawowa wurin sarki sai in ta gamshe shi, sai ya kuma kira ta da suna.
in the evening she has gone in, and in the morning she has turned back to the second house of the women, to the hand of Shaashgaz eunuch of the king, keeper of the concubines; she does not come in anymore to the king except the king has delighted in her, and she has been called by name.
15 Sa’ad da lokaci ya yi da Esta (yarinyar da Mordekai ya ɗauka tamƙar’yarsa,’yar kawunsa Abihayil) za tă shiga wurin sarki, ba tă nemi a ba ta kome ba in ban da abin da Hegai, bābān sarki mai lura da gidan matan kulle, ya ba da shawara. Esta kuwa ta sami tagomashin kowa da ya ganta.
And in the drawing near of the turn of Esther—daughter of Abihail, uncle of Mordecai, whom he had taken to himself for a daughter—to come in to the king, she has not sought a thing except that which Hegai eunuch of the king, keeper of the women, says, and Esther is receiving grace in the eyes of all seeing her.
16 Aka kai Esta wurin Sarki Zerzes a mazaunin sarauta a wata na goma, watan Tebet, a shekara ta bakwai ta mulkinsa.
And Esther is taken to King Ahasuerus, to his royal house, in the tenth month—it [is] the month of Tebeth—in the seventh year of his reign,
17 To, sarki ya so Esta fiye da duk sauran matan, ta kuma sami tagomashinsa da kuma yardarsa fiye da duk sauran budurwai. Saboda haka ya sa rawanin sarauta a kanta, ya kuma mai da ita sarauniya a maimakon Bashti.
and the king loves Esther above all the women, and she receives grace and kindness before him above all the virgins, and he sets a royal crown on her head, and causes her to reign instead of Vashti,
18 Sarki kuwa ya yi ƙasaitacciyar liyafa, liyafar Esta, wa dukan hakimansa da shugabannin masarautarsa. Ya yi shelar hutu ko’ina a larduna, ya kuma raba kyautai a yalwace irin na sarauta.
and the king makes a great banquet to all his heads and his servants—the banquet of Esther—and has made a release to the provinces, and gives gifts as a memorial of the king.
19 Sa’ad da aka tara budurwai karo na biyu, Mordekai kuwa yana zama a bakin ƙofar sarki.
And in the virgins being gathered a second time, then Mordecai is sitting in the gate of the king;
20 Amma Esta ta ɓoye asalin iyalinta da na al’ummarta yadda Mordekai ya ce ta yi, gama ta ci gaba da bin umarnan Mordekai yadda take yi sa’ad da yake renonta.
Esther is not declaring her family and her people, as Mordecai has laid a charge on her, and the saying of Mordecai Esther is doing as when she was truly with him.
21 Sa’ad da Mordekai yake zaune a bakin ƙofar sarki, sai Bigtana da Teresh, biyu daga cikin hafsoshin sarki masu gadin ƙofar shiga, suka yi fushi, suka kuma ƙulla su kashe sarki Zerzes.
In those days, when Mordecai is sitting in the gate of the king, has Bigthan been angry, and Teresh (two of the eunuchs of the king, the keepers of the threshold), and they seek to put forth a hand on King Ahasuerus,
22 Mordekai kuwa ya sami labarin makircin, ya kuma faɗa wa Sarauniya Esta, wadda ta faɗa wa sarki, ta kuma nuna masa cewa Mordekai ne ya ji.
and the thing is known to Mordecai, and he declares [it] to Esther the queen, and Esther speaks to the king in the name of Mordecai,
23 Sa’ad da aka bincika labarin aka kuma iske gaskiya ne, sai aka rataye hafsoshin nan biyu a wurin rataye mai laifi. Aka rubuta dukan wannan a cikin littafin tarihi a gaban sarki.
and the thing is sought out, and found, and both of them are hanged on a tree, and it is written in the scroll of the Chronicles before the king.