< Esta 2 >
1 Daga baya sa’ad da fushin Sarki Zerzes ya huce, sai ya tuna da Bashti da abin da ta yi, da kuma dokar da ya bayar game da ita.
After this, when the wrath of king Assuerus was appeased, he remembered Vasthi, and what she had done and what she had suffered:
2 Sai masu hidimar sarki na musamman, suka kawo shawara cewa, “Bari a nemi, kyawawan budurwai saboda sarki.
And the king’s servants and his officers said: Let young women be sought for the king, virgins and beautiful,
3 Bari sarki yă naɗa komishinoni a kowane yanki na masarautarsa, domin su kawo dukan waɗannan kyawawan’yan mata cikin harabar mazaunin masarautar a Shusha. Bari a sa su a hannun Hegai, bābān sarki, wanda yake lura da mata, bari kuma a yi musu kulawa ta musamman.
And let some persons be sent through all the provinces to look for beautiful maidens and virgins: and let them bring them to the city of Susan, and put them into the house of the women under the hand of Egeus the eunuch, who is the overseer and keeper of the king’s women: and let them receive women’s ornaments, and other things necessary for their use.
4 Sa’an nan bari yarinyar da ta gamshi sarki, tă zama sarauniya a maimakon Bashti.” Wannan shawara ta gamshi sarki, ya kuwa yi na’am da ita.
And whosoever among them all shall please the king’s eyes, let her be queen instead of Vasthi. The word pleased the king: and he commanded it should be done as they had suggested.
5 To, a cikin mazaunin masarauta a Shusha, akwai wani mutumin Yahuda, daga Kabilar Benyamin mai suna Mordekai, ɗan Yayir, ɗan Shimeyi, ɗan Kish,
There was a man in the city of Susan, a Jew, named Mardochai, the son of Jair, the son of Semei, the son of Cis, of the race of Jemini,
6 wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ɗauka tare’yan zaman bauta cikin waɗanda ya ɗauko daga Urushalima, tare da Yekoniya, sarkin Yahuda.
Who had been carried away from Jerusalem at the time that Nabuchodonosor king of Babylon carried away Jechonias king of Juda,
7 Mordekai yana da wata’yar kawunsa mai suna Hadassa, wanda ya yi reno, ba ta da mahaifi ko mahaifiya. Ita ce yarinyar da aka santa da suna Esta. Kyakkyawa ce ƙwarai. Mordekai dai ya ɗauke ta tamƙar’yarsa sa’ad da mahaifinta da mahaifiyarta suka mutu.
And he had brought up his brother’s daughter Edissa, who by another name was called Esther: now she had lost both her parents: and was exceeding fair and beautiful. And her father and mother being dead, Mardochai adopted her for his daughter.
8 Da aka yi shelar umarni da dokar sarki, sai aka kawo’yan mata masu yawa a mazaunin masarauta a Shusha, aka kuma sa su ƙarƙashin kulawar Hegai. Aka kawo Esta ma zuwa fadar sarki, aka danƙa ta wa Hegai, wanda yake lura da mata.
And when the king’s ordinance was noised abroad, and according to his commandment many beautiful virgins were brought to Susan, and were delivered to Egeus the eunuch: Esther also among the rest of the maidens was delivered to him to be kept in the number of the women.
9 Yarinyar ta gamshe shi, ta kuma sami tagomashinsa. Nan da nan ya tanada mata, ya ba ta man shafawa da abinci na musamman. Ya ba ta bayi mata bakwai da aka zaɓa daga fadar sarki. Ya kuma kai ta tare da bayinta zuwa wuri mafi kyau na gidan matan kulle.
And she pleased him, and found favour in his sight. And he commanded the eunuch to hasten the women’s ornaments, and to deliver to her her part, and seven of the most beautiful maidens of the king’s house, and to adorn and deck out both her and her waiting maids.
10 Esta ba tă bayyana asalin al’ummarta da na iyalinta ba, domin Mordekai ya hana yin haka.
And she would not tell him her people nor her country. For Mardochai had charged her to say nothing at all of that:
11 Kowace rana Mordekai yana kai da komowa kusa da harabar filin gidan matan kulle, domin ya san yadda Esta take, da kuma abin da yake faruwa da ita.
And he walked every day before the court of the house, in which the chosen virgins were kept, having a care for Esther’s welfare, and desiring to know what would befall her.
12 Kafin a kai kowace yarinya wurin Sarki Zerzes, sai ta gama watanni goma sha biyu cif ana yin mata kwalliyar da aka tsara, akan ɗauki watanni shida ana shafa mata man mur, a ɗauki watanni shida kuma ana shafa mata man ƙanshi da kayan shafe-shafe.
Now when every virgin’s turn came to go in to the king, after all had been done for setting them off to advantage, it was the twelfth month: so that for six months they were anointed with oil of myrrh, and for other six months they used certain perfumes and sweet spices.
13 A kuma koya mata yadda za tă tafi wurin sarki. Aka ba ta duk abin da take so ta riƙe daga gidan matan kulle zuwa fadar sarki.
And when they were going in to the king, whatsoever they asked to adorn themselves they received: and being decked out, as it pleased them, they passed from the chamber of the women to the king’s chamber.
14 Da yamma za tă tafi can, da safe kuma ta dawo wani ɓangaren gidan matan kullen da yake a ƙarƙashin kulawar Sha’ashgaz, bābā na sarki, wanda yake lura da ƙwarƙwarai. Ba ta dawowa wurin sarki sai in ta gamshe shi, sai ya kuma kira ta da suna.
And she that went in at evening, came out in the morning, and from thence she was conducted to the second house, that was under the hand of Susagaz the eunuch, who had the charge over the king’s concubines: neither could she return any more to the king, unless the king desired it, and had ordered her by name to come.
15 Sa’ad da lokaci ya yi da Esta (yarinyar da Mordekai ya ɗauka tamƙar’yarsa,’yar kawunsa Abihayil) za tă shiga wurin sarki, ba tă nemi a ba ta kome ba in ban da abin da Hegai, bābān sarki mai lura da gidan matan kulle, ya ba da shawara. Esta kuwa ta sami tagomashin kowa da ya ganta.
And as the time came orderly about, the day was at hand, when Esther, the daughter of Abihail the brother of Mardochai, whom he had adopted for his daughter, was to go in to the king. But she sought not women’s ornaments, but whatsoever Egeus the eunuch the keeper of the virgins had a mind, he gave her to adorn her. For she was exceeding fair, and her incredible beauty made her appear agreeable and amiable in the eyes of all.
16 Aka kai Esta wurin Sarki Zerzes a mazaunin sarauta a wata na goma, watan Tebet, a shekara ta bakwai ta mulkinsa.
So she was brought to the chamber of king Assuerus the tenth month, which is called Tebeth, in the seventh year of his reign.
17 To, sarki ya so Esta fiye da duk sauran matan, ta kuma sami tagomashinsa da kuma yardarsa fiye da duk sauran budurwai. Saboda haka ya sa rawanin sarauta a kanta, ya kuma mai da ita sarauniya a maimakon Bashti.
And the king loved her more than all the women, and she had favour and kindness before him above all the women, and he set the royal crown on her head, and made her queen instead of Vasthi.
18 Sarki kuwa ya yi ƙasaitacciyar liyafa, liyafar Esta, wa dukan hakimansa da shugabannin masarautarsa. Ya yi shelar hutu ko’ina a larduna, ya kuma raba kyautai a yalwace irin na sarauta.
And he commanded a magnificent feast to be prepared for all the princes, and for his servants, for the marriage and wedding of Esther. And he gave rest to all the provinces, and bestowed gifts according to princely magnificence.
19 Sa’ad da aka tara budurwai karo na biyu, Mordekai kuwa yana zama a bakin ƙofar sarki.
And when the virgins were sought the second time, and gathered together, Mardochai stayed at the king’s gate,
20 Amma Esta ta ɓoye asalin iyalinta da na al’ummarta yadda Mordekai ya ce ta yi, gama ta ci gaba da bin umarnan Mordekai yadda take yi sa’ad da yake renonta.
Neither had Esther as yet declared her country and people, according to his commandment. For whatsoever he commanded, Esther observed: and she did all things in the same manner as she was wont at that time when he brought her up a little one.
21 Sa’ad da Mordekai yake zaune a bakin ƙofar sarki, sai Bigtana da Teresh, biyu daga cikin hafsoshin sarki masu gadin ƙofar shiga, suka yi fushi, suka kuma ƙulla su kashe sarki Zerzes.
At that time, therefore, when Mardochai abode at the king’s gate, Bagathan and Thares, two of the king’s eunuchs, who were porters, and presided in the first entry of the palace, were angry: and they designed to rise up against the king, and to kill him.
22 Mordekai kuwa ya sami labarin makircin, ya kuma faɗa wa Sarauniya Esta, wadda ta faɗa wa sarki, ta kuma nuna masa cewa Mordekai ne ya ji.
And Mardochai had notice of it, and immediately he told it to queen Esther: and she to the king in Mardochai’s name, who had reported the thing unto her.
23 Sa’ad da aka bincika labarin aka kuma iske gaskiya ne, sai aka rataye hafsoshin nan biyu a wurin rataye mai laifi. Aka rubuta dukan wannan a cikin littafin tarihi a gaban sarki.
It was inquired into, and found out: and they were both hanged on a gibbet. And it was put in the histories, and recorded in the chronicles before the king.