< Esta 1 >

1 Ga abin da ya faru a zamanin Zerzes. Zerzes ya yi mulki bisan larduna 127 daga Indiya zuwa Kush.
I KE kau ia Ahasuero, (o Ahasuero ia i alii ai maluna o na aina hookahi haneri me ka iwakaluakumamahiku, mai Inia mai a Aitiopia: )
2 A lokacin nan, Sarki Zerzes ya yi mulki daga gadon sarauta, cikin mazaunin masarautar Shusha.
Ia manawa, i ka wa e noho ana o Ahasuero ke alii maluna o ka nohoalii o kona aupuni, aia ma Susana ka pakaua;
3 A shekara ta uku ta mulkinsa, ya yi wa dukan hakimansa da ma’aikatansa liyafa. Shugabannin mayaƙan Farisa, da Mediya, da yerimai; da kuma hakimai na lardunan suka kasance.
I ke kolu o ka makahiki o kona nohoalii ana, hana iho la ia i ahaaina na kona poe alii a pau, a me kana poe kauwa; a aia hoi imua ona ka poe koa o Peresia a me Media, o na kaukaualii hoi, a me na'lii o na aina:
4 Kwanaki 180 cif, ya nuna yawan dukiyar masarautarsa, da ɗaukakarta da kuma darajar girmansa.
A hoike oia i ka waiwai nani o kona aupuni, a me ka hanohauo o kona maikai nui, no na la he nui loa, hookahi haneri a me kanawalu mau la.
5 Sa’ad da waɗannan kwanaki suka wuce, sai sarki ya yi liyafa a cikin lambun da aka shinge na fadar sarki wadda ta ɗauki kwana bakwai wa dukan mutane daga ƙarami har zuwa babba, waɗanda suke zama a masarautar Shusha.
A hala ia mau la, alaila, hana iho la ke alii i ahaaina, i ehiku la, ma ke kahua pakaua o ka hale o ke alii, no na mea a pau i loaa ma Susana ka pakaua, no na mea koikoi a me na makaainana.
6 Lambun yana da fararen labulen da aka rataye da shunayya na lallausan lilin, da aka ɗaura da igiyoyin fararen lilin, da yadin jan garura, haɗe da zoban azurfa a kan ginshiƙin farin ƙasa. A nan, akwai kujeru na zinariya da na azurfa a kan daɓe mai ado da aka yi da duwatsu masu daraja, da farin ƙasa, da fararen duwatsun wuya, da waɗansu duwatsu masu tsada.
O na paku hoi, he lole huluhulu keokeo, a he olona keokeo, a me ka poni, ua paa i na kaula huluhulu keokeo, maikai, a me ka ulaula, i nakiia iloko o na komo dala, ma na kia pohaku keokeo. O na noho hilinai, he gula ia a me ke kala maluna o ke kahua pohaku omaomao, a keokeo, i hoonoho pu ia me na momi a me ka ea.
7 Aka rarraba ruwan inabi cikin kwaf na zinariya, kowanne kuwa dabam yake da ɗayan. Ruwan inabin kuwa yana da yawa, bisa ga wadatar sarki.
Haawi lakou i ka mea inu maloko o na kiaha gula, a ua like ole kekahi kiaha me kekahi kiaha, a ua nui ka waina maikai, e like me ka aoao mau o ke alii.
8 Bisa ga umarnin sarki, aka bar kowane baƙo yă sha yadda ya ga dama, gama sarki ya umarci dukan bayin da suke rarraba ruwan inabin su ba wa kowa abin da yake so.
Mamuli o ke kanawai ka inu ana, aole mea nana i koi aku; no ka mea, pela ke kauoha a ke alii i na luna a pau o kona hale, e hana kela kanaka keia kanaka e like me kona manao iho.
9 Sarauniya Bashti ita ma ta yi liyafa saboda mata a fadar Sarki Zerzes.
O Vaseti, ke alii wahine kekahi, hana iho la oia i ahaaina na na wahine ma ka halealii o ke alii o Ahasuero.
10 A rana ta bakwai, sa’ad da Sarki Zerzes, ya yi tilis da ruwan inabi, sai ya umarci bābānni bakwai waɗanda suke yin masa hidima, wato, Mehuman, Bizta, Harbona, Bigta, Abagta, Zetar da Karkas,
A i ka hiku o ka la, i ka wa i olioli ai ka naau o ke alii i ka waina, olelo ae la ia ia Mehumana, a me Bizeta, a me Harebona, a me Bigeta, a me Abageta, a me Zetara, a me Karekasa, na luna ehiku i hookauwa ma ke alo o ke alii, o Ahasuero,
11 su kawo Sarauniya Bashti a gabansa, sanye da rawanin sarautarta, don ta nuna kyanta wa mutane da kuma hakimai, gama ita kyakkyawa ce ƙwarai.
E lawe mai lakou ia Vaseti, i ke alii wahine imua i ke alo o ke alii, me ka papale alii, e hoike aku i na kanaka a me na'lii, i kona maikai; no ka mea, he helehelena maikai kona.
12 Amma da masu hidima suka ba da umarnin sarki, sai Sarauniya Bashti ta ƙi zuwa. Wannan ya ɓata wa sarki rai, ya kuma yi fushi ƙwarai.
Hoole ae la ke alii wahine, o Vaseti, aole e hele ma ka olelo a ke alii, ana i kauoha ae i na luna. Nolaila, ukiuki loa iho la ke alii, a wela iho la kona huhu iloko ona.
13 Da yake, al’ada ce sarki yă nemi shawara daga sanannu a batun doka da adalci, sai ya yi magana da masu hikima waɗanda suke fahimtar lokuta
Alaila, olelo ae la ke alii i ka poe akamai, i ka poe i ike i na manawa, (no ka mea, pela no ke alii i hana'i imua i ke alo o ka poe a pau i ike i ke kanawai a me ka hooponopono:
14 suke kuma mafi kusa da sarki. Waɗannan masu hikima kuwa su ne, Karshena, Shetar, Admata, Tarshish, Meres, Marsena da kuma Memukan. Su hakimai bakwai ne na Farisa da Mediya waɗanda suke da dama ta musamman ta kaiwa ga sarki, suke kuma da matsayi mafi girma a masarautar.
Eia ka poe i pili ia ia, o Karesena, o Setara, o Ademata, o Taresisa, o Meresa, o Maresena, a me Memukana, ehiku alii o Peresia, a me Media, a ike lakou i ka maka o ke alii, a o lakou na mea noho kiekie maloko o ke aupuni: )
15 Ya ce, “Bisa ga doka, me za a yi wa Sarauniya Bashti? Gama ta ƙi yin biyayya da umarnin sarki Zerzes da bābānni suka kai mata?”
Mamuli o ke kanawai, pehea la kakou e hana'i i ke alii wahine ia Vaseti, no kona malama ole ana i ka olelo a ke alii, a Ahasuero, ma ka lima o na luna?
16 Sai Memukan ya amsa a gaban sarki da hakimai ya ce, “Sarauniya Bashti ta yi laifi, ba ga sarki kaɗai ba, amma ga dukan hakimai ma, da kuma mutanen dukan lardunan sarki Zerzes.
Alaila, olelo aku la o Memukana imua i ke alo o ke alii, a me na'lii, Ua hana hewa o Vaseti ke alii wahine, aole i ke alii wale no, aka, i na'lii a pau, a me na kanaka a pau e noho ana ma na aina a pau o Ke alii o Ahasuero.
17 Domin halin Sarauniya zai zama sananne ga dukan mata, ta haka kuwa za su ƙasƙantar da mazansu su kuma ce, ‘Sarki Zerzes ya umarta a kawo Sarauniya Bashti a gabansa, amma ta ƙi zuwa.’
No ka mea, e kaulana aku no ia hana a ke alii wahine, i na wahine a pau, nolaila, e hoowahawahaia'i ka lakou poe kane e lakou, i ka wa e kaulana'i ke kanoha ana a ke alii a Ahasuero e laweia mai imua ona o Vaseti ke alii wahine, aole ia i hele mai.
18 Wannan rana matan hakiman Farisa da na Mediya waɗanda suka ji game da halin sarauniya, za su yi haka wa dukan hakiman sarki. Zai zama babu ƙarshen rashin bangirma da kuma reni.
A i keia la, o na'lii wahine a pau o Peresia, a me Media, ka poe i lohe i ka nana a ke alii wahine, e olelo no lakou pela i na kuhina o ke alii. Pela e nui loa ai auanei ka hoowahawaha ana, a me ka ukiuki.
19 “Saboda haka, in ya gamshi sarki, bari yă ba da hatimi na sarauta, bari kuma a rubuta shi cikin dokokin Farisa da Mediya, wanda ba za a iya sokewa ba, cewa Bashti ba za tă ƙara zuwa gaban sarkin Zerzes ba. Bari kuma sarki yă ba da matsayinta na sarauta ga wata, wadda ta fi ta.
Ina he maikai i ko ke alii manao, e hoolahaia'ku no kekahi olelo no ke aupuni, a e kakauia no hoi ia ma na kanawai o Peresia a me Media, i haule ole ia, aole loa e hele hou mai o Vaseti imua i ke alo o ke alii, o Ahasuero; a e haawi aku hoi ke alii i ko Vaseti waiwai alii na kekahi i oi aku ka pono mamua o kona.
20 Ta haka, sa’ad da aka yi shelar dokar sarki ko’ina a fāɗin masarautarsa, dukan mata za su ba wa mazansu girma, daga ƙarami har zuwa babba.”
Aia hoolahaia ke kanawai a ke alii e hana'i, ma kona aupuni a pau, (no ka mea he nui ia, ) alaila e hoomaikai no na wahine i ka lakou poe kane i na mea nui a me na mea uuku.
21 Sarki da hakimansa suka gamsu da wannan shawara. Saboda haka sarki ya yi kamar yadda Memukan ya faɗa.
Ua maikai keia olelo i ka manao o ke alii, a me na kuhina, a hana iho la ke alii e like me ka olelo a Memukana.
22 Ya aika da saƙo zuwa ga dukan ɓangarorin masarautar, zuwa ga kowane lardi a irin nasa rubutu, zuwa kuma ga kowane mutane a nasu harshe, ana shelar a kowane yare na mutane, cewa kowane mutum yă zama mai mulki bisa gidansa.
A hoouna ae la ia i na palapala i na mokuna a pau o ke alii, i kela mokuna i keia mokuna, e like me ka mea i palapalaia, a i kela lahuikanaka i keia lahuikanaka, e like me ka lakou olelo iho, e noho haku no kela kanaka keia kanaka ma kona hale iho; a hoolahaia'ku la keia ma ka olelo o na lahuikanakaa pau.

< Esta 1 >