< Afisawa 1 >

1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
Paulus, ein Apostel Jesu Christi durch den Willen Gottes, an die Heiligen zu Ephesus und Gläubigen an Jesus Christus:
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Gnade sei mit euch und Friede von Gott unserem Vater und dem Herrn Jesus Christus.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Gelobt sei Gott und der Vater unseres Herrn Jesus Christus, Der uns mit allerlei geistigen Segnungen an himmlischen Gütern durch Christus gesegnet hat.
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
Wie Er uns denn erwählt hat durch Ihn, vor Gründung der Welt, damit wir heilig und tadellos wären vor Ihm in der Liebe.
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
Indem Er uns vorherbestimmt hat zur Kindschaft durch Jesus Christus für Ihn Selbst nach dem Wohlgefallen Seines Willens;
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
Zum Lob der Herrlichkeit Seiner Gnade, womit Er uns begnadigt hat in dem Geliebten;
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
An Dem wir haben die Erlösung durch Sein Blut, die Vergebung der Sünden,
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
Nach dem Reichtum Seiner Gnade, die uns überschwenglich zuteil wurde in jeglicher Weisheit und Einsicht;
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
Indem Er uns das Geheimnis Seines Willens nach Seinem Wohlgefallen kund tat, nach welchem Er bei Sich beschlossen hatte,
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
In Hinsicht auf die Veranstaltung der Erfüllung der Zeiten, alles im Himmel und auf Erden in Christus zusammenzufassen,
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
In Ihm, durch Den wir auch zum Erbteil gekommen, die wir zuvor verordnet sind nach dem Ratschlusse Dessen, Der alle Dinge wirkt nach dem Rat Seines Willens;
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
Auf daß wir zum Lobe Seiner Herrlichkeit dienten, die wir zuvor auf Christus gehofft haben.
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
In Dem auch ihr, da ihr das Wort der Wahrheit, das Evangelium eures Heils gehört und an Ihn geglaubt habt, versiegelt worden seid mit dem Heiligen Geiste der Verheißung;
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
Welcher ist das Pfand unseres Erbes, auf die Erlösung des Eigentums zum Preis Seiner Herrlichkeit.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
Darum auch ich, nachdem ich von eurem Glauben an den Herrn Jesus bei euch, und von eurer Liebe zu allen Heiligen gehört habe,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
Nicht aufhöre zu danken für euch, indem ich euer in meinem Gebete gedenke.
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
Daß der Gott unseres Herrn Jesus Christus, der Vater der Herrlichkeit, euch gebe den Geist der Weisheit und der Offenbarung zu Seiner Erkenntnis;
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
Und erleuchte die Augen eures Verständnisses, auf daß ihr seht, welches da ist die Hoffnung Seiner Berufung, und welches da ist der Reichtum der Herrlichkeit Seines Erbes unter den Heiligen,
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
Und welches da ist die überschwengliche Größe Seiner Macht an uns, die wir glauben vermöge der Wirksamkeit Seiner gewaltigen Kraft,
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
Die Er in Christus gewirkt hat, da Er Ihn von den Toten auferweckt und zu Seiner Rechten im Himmel gesetzt hat.
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn g165)
Hoch über alle Obrigkeit und Gewalt, Macht, Herrschaft, und über alle Namen, die genannt werden mögen, nicht allein in dieser Welt, sondern auch in der zukünftigen, (aiōn g165)
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
Und hat alle Dinge unter Seine Füße gelegt, und Ihn zum Haupt gesetzt über alles in der Gemeinde,
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
Welche ist Sein Leib und die Fülle Dessen, Der alles in allem erfüllt.

< Afisawa 1 >