< Afisawa 1 >
1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
Paul, an Apostle of Jesus Christ through the will of God, to all the saints who are at Ephesus and to the faithful in Christ Jesus.
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace and peace to you from God the Father, and from the Lord Jesus Christ.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, who has blessed us with every spiritual blessing in the heavens, in Christ,
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
just as he chose us in him before the foundation of the world, so that we would be holy and immaculate in his sight, in charity.
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
He has predestined us to adoption as sons, through Jesus Christ, in himself, according to the purpose of his will,
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
for the praise of the glory of his grace, with which he has gifted us in his beloved Son.
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
In him, we have redemption through his blood: the remission of sins in accord with the riches of his grace,
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
which is superabundant in us, with all wisdom and prudence.
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
So does he make known to us the mystery of his will, which he has set forth in Christ, in a manner well-pleasing to him,
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
in the dispensation of the fullness of time, so as to renew in Christ everything that exists through him in heaven and on earth.
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
In him, we too are called to our portion, having been predestined in accord with the plan of the One who accomplishes all things by the counsel of his will.
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
So may we be, to the praise of his glory, we who have hoped beforehand in Christ.
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
In him, you also, after you heard and believed the Word of truth, which is the Gospel of your salvation, were sealed with the Holy Spirit of the Promise.
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
He is the pledge of our inheritance, unto the acquisition of redemption, to the praise of his glory.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
Because of this, and hearing of your faith that is in the Lord Jesus, and of your love toward all the saints,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
I have not ceased giving thanks for you, calling you to mind in my prayers,
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
so that the God of our Lord Jesus Christ, the Father of glory, may give a spirit of wisdom and of revelation to you, in knowledge of him.
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
May the eyes of your heart be illuminated, so that you may know what is the hope of his calling, and the wealth of the glory of his inheritance with the saints,
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
and the preeminent magnitude of his virtue toward us, toward we who believe in accord with the work of his powerful virtue,
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
which he wrought in Christ, raising him from the dead and establishing him at his right hand in the heavens,
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn )
above every principality and power and virtue and dominion, and above every name that is given, not only in this age, but even in the future age. (aiōn )
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
And he has subjected all things under his feet, and he has made him the head over the entire Church,
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
which is his body and which is the fullness of him who accomplishes everything in everyone.