< Afisawa 1 >

1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
Paulus, Kristi Jesu Apostel ved Guds Villie, til de hellige, som ere i Efesus og ere troende i Kristus Jesus:
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Nåde være med eder og Fred fra Gud vor Fader og den Herre Jesus Kristus!
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Lovet være Gud og vor Herres Jesu Kristi Fader, som har velsignet os med al åndelig Velsignelse i det himmelske i Kristus,
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
ligesom han har udvalgt os i ham før Verdens Grundlæggelse til at være hellige og ulastelige for hans Åsyn,
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
idet han i Kærlighed forudbestemte os til Sønneudkårelse hos sig ved Jesus Kristus, efter sin Villies Velbehag,
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
til Pris for sin Nådes Herlighed, som han benådede os med i den elskede,
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
i hvem vi have Forløsningen ved hans Blod, Syndernes Forladelse, efter hans Nådes Rigdom,
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
som han rigelig tildelte os i al Visdom og Forstand,
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
idet han kundgjorde os sin Villies Hemmelighed, efter sin velbehagelige Beslutning, som han havde fattet hos sig selv,
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
for at oprette en Husholdning i Tidernes Fylde, nemlig at sammenfatte sig alt i Kristus, det, som er i Himlene, og det, som er på Jorden, i ham,
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
i hvem vi også have fået Arvelodden, forud bestemte efter hans Forsæt, der virker alt efter sin Villies Råd,
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
for at vi skulde være til Pris for hans Herlighed, vi, som forud havde håbet på Kristus,
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
i hvem også I, da I hørte Sandhedens Ord, Evangeliet om eders Frelse, i hvem I også, da I bleve troende, bleve beseglede med Forjættelsens hellige Ånd,
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
som er Pant på vor Arv, til Ejendommens Forløsning, til Pris for hans Herlighed.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
derfor har også jeg, efter at have hørt om eders Tro på den Herre Jesus og om eders Kærlighed til alle de hellige,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
ikke ophørt at takke for eder, idet jeg ihukommer eder i mine Bønner om,
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
at vor Herres Jesu Kristi Gud, Herlighedens Fader, må give eder Visdoms og Åbenbarelses Ånd i Erkendelse af ham,
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
gøre eders Hjertes Øjne oplyste til at kende, hvilket det Håb er, som han kaldte eder til, hvilken hans Arvs Herligheds Rigdom er iblandt de hellige,
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
og hvilken hans Krafts overvættes Storhed er over for os, som tro, alt efter hans Styrkes vældige Virkekraft,
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
som han udviste på Kristus, da han oprejste ham fra de døde og satte ham ved sin højre Hånd i det himmelske,
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn g165)
langt over al Magt og Myndighed og Kraft og Herredom og hvert Navn, som nævnes, ikke alene i denne Verden, men også i den kommende, (aiōn g165)
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
og lagde alt under hans Fødder, og ham gav han som Hoved over alting til Menigheden,
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
der er hans Legeme, fyldt af ham, som fylder alt i alle.

< Afisawa 1 >