< Afisawa 1 >

1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
ܦܘܠܘܤ ܫܠܝܚܐ ܕܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ ܒܨܒܝܢܗ ܕܐܠܗܐ ܠܐܝܠܝܢ ܕܐܝܬܝܗܘܢ ܒܐܦܤܘܤ ܩܕܝܫܐ ܘܡܗܝܡܢܐ ܒܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
ܫܠܡܐ ܥܡܟܘܢ ܘܛܝܒܘܬܐ ܡܢ ܐܠܗܐ ܐܒܘܢ ܘܡܢ ܡܪܢ ܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
ܡܒܪܟ ܗܘ ܐܠܗܐ ܐܒܘܗܝ ܕܡܪܢ ܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ ܗܘ ܕܒܪܟܢ ܒܟܠ ܒܘܪܟܢ ܕܪܘܚ ܒܫܡܝܐ ܒܡܫܝܚܐ
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
ܐܝܟܢܐ ܕܩܕܡ ܓܒܢ ܒܗ ܡܢ ܩܕܡ ܬܪܡܝܬܗ ܕܥܠܡܐ ܕܢܗܘܐ ܩܕܝܫܐ ܘܕܠܐ ܡܘܡ ܩܕܡܘܗܝ ܘܒܚܘܒܐ ܩܕܡ ܪܫܡܢ ܠܗ
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
ܘܤܡܢ ܠܒܢܝܐ ܒܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ ܐܝܟ ܕܫܦܪ ܠܨܒܝܢܗ
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
ܕܢܫܬܒܚ ܫܘܒܚܐ ܕܛܝܒܘܬܗ ܗܘ ܕܐܫܦܥ ܥܠܝܢ ܒܝܕ ܚܒܝܒܗ
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
ܕܒܗ ܐܝܬ ܠܢ ܦܘܪܩܢܐ ܘܒܕܡܗ ܫܘܒܩܢܐ ܕܚܛܗܐ ܐܝܟ ܥܘܬܪܐ ܕܛܝܒܘܬܗ
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
ܗܝ ܕܐܬܝܬܪܬ ܒܢ ܒܟܠ ܚܟܡܐ ܘܒܟܠ ܤܘܟܠ
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
ܘܐܘܕܥܢ ܐܪܙܐ ܕܨܒܝܢܗ ܗܘ ܕܩܕܡ ܗܘܐ ܤܡ ܕܢܤܥܘܪ ܒܗ
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
ܠܡܕܒܪܢܘܬܐ ܕܡܘܠܝܗܘܢ ܕܙܒܢܐ ܕܟܠܡܕܡ ܡܢ ܕܪܝܫ ܢܬܚܕܬ ܒܡܫܝܚܐ ܕܒܫܡܝܐ ܘܒܐܪܥܐ
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
ܘܒܗ ܚܢܢ ܐܬܓܒܝܢ ܐܝܟ ܕܩܕܡ ܪܫܡܢ ܘܨܒܐ ܗܘ ܕܟܠ ܤܥܪ ܐܝܟ ܬܪܥܝܬܐ ܕܨܒܝܢܗ
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
ܕܢܗܘܐ ܚܢܢ ܐܝܠܝܢ ܕܩܕܡܢ ܤܒܪܢ ܒܡܫܝܚܐ ܠܗܕܪܐ ܕܬܫܒܘܚܬܗ
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
ܕܐܦ ܐܢܬܘܢ ܒܗ ܫܡܥܬܘܢ ܡܠܬܐ ܕܩܘܫܬܐ ܕܐܝܬܝܗ ܤܒܪܬܐ ܕܚܝܝܟܘܢ ܘܒܗ ܗܝܡܢܬܘܢ ܘܐܬܚܬܡܬܘܢ ܒܪܘܚܐ ܕܩܘܕܫܐ ܕܡܠܝܟܐ ܗܘܬ
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
ܗܝ ܕܐܝܬܝܗ ܪܗܒܘܢܐ ܕܝܪܬܘܬܢ ܠܦܘܪܩܢܐ ܕܐܝܠܝܢ ܕܚܐܝܢ ܘܠܫܘܒܚܐ ܕܐܝܩܪܗ
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
ܡܛܠ ܗܢܐ ܐܦ ܐܢܐ ܗܐ ܡܢ ܕܫܡܥܬ ܗܝܡܢܘܬܟܘܢ ܕܒܡܪܢ ܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ ܘܚܘܒܟܘܢ ܕܠܘܬ ܩܕܝܫܐ
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
ܠܐ ܡܫܬܠܐ ܐܢܐ ܠܡܘܕܝܘ ܥܠ ܐܦܝܟܘܢ ܘܠܡܥܗܕܟܘܢ ܒܨܠܘܬܝ
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
ܕܐܠܗܗ ܕܡܪܢ ܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ ܐܒܐ ܕܬܫܒܘܚܬܐ ܢܬܠ ܠܟܘܢ ܪܘܚܐ ܕܚܟܡܬܐ ܘܕܓܠܝܢܐ ܒܝܕܥܬܗ
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
ܘܢܢܗܪܢ ܥܝܢܐ ܕܠܒܘܬܟܘܢ ܕܬܕܥܘܢ ܡܢܘ ܤܒܪܐ ܕܩܪܝܢܗ ܘܡܢܘ ܥܘܬܪܐ ܕܫܘܒܚܐ ܕܝܪܬܘܬܗ ܒܩܕܝܫܐ
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
ܘܡܢܐ ܗܝ ܝܬܝܪܘܬܐ ܕܪܒܘܬܐ ܕܚܝܠܗ ܒܢ ܒܐܝܠܝܢ ܕܡܗܝܡܢܝܢܢ ܐܝܟ ܡܥܒܕܢܘܬܐ ܕܬܘܩܦܐ ܕܚܝܠܗ
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
ܕܥܒܕ ܒܡܫܝܚܐ ܘܐܩܝܡܗ ܡܢ ܒܝܬ ܡܝܬܐ ܘܐܘܬܒܗ ܡܢ ܝܡܝܢܗ ܒܫܡܝܐ
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn g165)
ܠܥܠ ܡܢ ܟܠܗܝܢ ܐܪܟܘܤ ܘܫܘܠܛܢܐ ܘܚܝܠܐ ܘܡܪܘܬܐ ܘܠܥܠ ܡܢ ܟܠ ܫܡ ܕܡܫܬܡܗ ܠܐ ܒܠܚܘܕ ܒܥܠܡܐ ܗܢܐ ܐܠܐ ܐܦ ܒܕܥܬܝܕ (aiōn g165)
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
ܘܫܥܒܕ ܟܠܡܕܡ ܬܚܝܬ ܪܓܠܘܗܝ ܘܠܗ ܕܐܝܬܘܗܝ ܠܥܠ ܡܢ ܟܠ ܝܗܒܗ ܪܫܐ ܠܥܕܬܐ
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
ܕܐܝܬܝܗ ܓܘܫܡܗ ܘܫܘܡܠܝܐ ܕܗܘ ܕܟܠ ܒܟܠ ܡܫܡܠܐ

< Afisawa 1 >