< Afisawa 6 >

1 Ku’ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku, gama ku na Ubangiji, abin da ya dace ku yi ke nan.
Children, obey your parents in the Lord, for this is right.
2 Doka ta farko wadda aka haɗa da alkawari ita ce, “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,
"Honor your father and mother," which is the first commandment with a promise:
3 don ka zauna lafiya, ka kuma yi tsawon rai a duniya.”
"that it may be well with you, and that you may live long in the land."
4 Ku kuma iyaye, kada ku tsokane’ya’yanku. Ku yi musu reno mai kyau. Ku koyar da su, ku kuma gargaɗe su game da Ubangiji.
And fathers, do not provoke your children to anger, but nurture them in the discipline and instruction of the Lord.
5 Ku bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya. Ku nuna musu halin bangirma, kuna kuma yin musu biyayya cikin dukan abu, da zuciya ɗaya kamar ga Kiristi kuke yi.
Servants, be obedient to those who according to the flesh are your masters, with fear and trembling, in singleness of your heart, as to Christ;
6 Ku yi aiki sosai, ba don kawai ku gamshe su sa’ad da suke kallonku ba. Da yake ku bayin Kiristi ne, ku aikata nufin Allah da dukan zuciyarku.
not in the way of service only when eyes are on you, as people-pleasers; but as servants of Christ, doing the will of God from the heart;
7 Ku yi aikinku da kyakkyawar niyya, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba mutane ba.
with good will doing service, as to the Lord, and not to people;
8 Gama kun san cewa Ubangiji zai ba da lada ga kowa gwargwadon kowane aiki nagarin da ya yi, ko shi bawa ne, ko’yantacce.
knowing that whatever good thing each one does, he will receive the same again from the Lord, whether he is bound or free.
9 Ku kuma masu bayi, dole ku bi da bayinku da kyau. Ku daina ba su tsoro. Ku tuna, ku da su, Maigida ɗaya kuke da shi a sama, kuma ba ya nuna bambanci.
You masters, do the same things to them, and give up threatening, knowing that he who is both their Master and yours is in heaven, and there is no partiality with him.
10 A ƙarshe, bari ƙarfin ikon Ubangiji yă ba ku ƙarfi.
Finally, be strong in the Lord, and in the strength of his might.
11 Ku yafa dukan kayan yaƙin da Allah yake bayarwa, don ku iya kāre kanku daga dabarun Shaiɗan.
Put on the whole armor of God, that you may be able to stand against the schemes of the devil.
12 Gama ba da mutane da suke nama da jini ne muke yaƙi ba. Muna yaƙi ne da ikoki, da hukumomi, da masu mulkin duhu, da kuma a ikokin da suke cikin a sararin sama. (aiōn g165)
For our wrestling is not against flesh and blood, but against the rulers, against the powers, against the world's rulers of this darkness, and against the spiritual forces of wickedness in the heavenly places. (aiōn g165)
13 Saboda haka sai ku yafa dukan kayan yaƙi na Allah, domin sa’ad da ranar mugun nan ta zo, ku iya yin tsayin daka, bayan kuma kuka gama kome, ku dāge.
Therefore, put on the whole armor of God, that you may be able to withstand in the evil day, and, having done all, to stand.
14 Saboda haka fa ku dāge, ku sa gaskiya tă zama ɗamararku, adalci yă zama sulkenku,
Stand therefore, having the belt of truth buckled around your waist, and having put on the breastplate of righteousness,
15 shirin kai bisharar salama yă zama kamar takalmi a ƙafafunku.
and having fitted your feet with the preparation of the Good News of peace;
16 Ban da waɗannan kuma, ku ɗauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku iya kashe dukan kibiyoyin wutar Mugun nan da ita.
above all, taking up the shield of faith, with which you will be able to quench all the fiery darts of the evil one.
17 Ku kuma ɗauki hular kwano na ceto, da takobin Ruhu, wato, Maganar Allah.
And take the helmet of salvation, and the sword of the Spirit, which is the spoken word of God;
18 A koyaushe ku kasance kuna addu’a da roƙo ta wurin ikon Ruhu ba fasawa. A kan wannan manufa ku zauna a faɗake da matuƙar naci, kuna yin wa dukan mutanen Ubangiji addu’a.
with all prayer and requests, praying at all times in the Spirit, and being watchful to this end in all perseverance and requests for all the saints:
19 Ku kuma yi addu’a domina, don duk sa’ad da na buɗe bakina, in sami kalmomi babu tsoro, don in sanar da asirin bishara,
on my behalf, that utterance may be given to me in opening my mouth, to make known with boldness the mystery of the Good News,
20 wadda nake jakadanta cikin sarƙoƙi. Ku yi addu’a don in iya yin shelarta babu tsoro, yadda ya kamata in yi.
for which I am an ambassador in chains; that in it I may speak boldly, as I ought to speak.
21 Tikikus, ƙaunataccen ɗan’uwa da kuma amintaccen bawa cikin Ubangiji, zai faɗa muku kome, domin ku ma ku san yadda nake, da kuma abin da nake yi.
But that you also may know my affairs, how I am doing, Tychicus, the beloved brother and faithful servant in the Lord, will make known to you all things;
22 Na aike shi gare ku musamman don wannan, domin ku san yadda muke, yă kuma ƙarfafa ku.
whom I have sent to you for this very purpose, that you may know our state, and that he may comfort your hearts.
23 ’Yan’uwa, salama tare da ƙauna da kuma bangaskiya daga Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi su kasance tare da ku.
Peace be to the brothers, and love with faith, from God the Father and the Lord Jesus Christ.
24 Alheri yă tabbata ga dukan masu ƙaunar Ubangiji Yesu Kiristi da ƙauna marar ƙarewa.
Grace be with all those who love our Lord Jesus Christ with incorruptible love.

< Afisawa 6 >