< Afisawa 5 >

1 Ku zama masu koyi da Allah, kamar ƙaunatattun’ya’ya,
Imitad entonces a Dios, pues que sois sus, hijos amados;
2 ku kuma yi rayuwar ƙauna, kamar yadda Kiristi ya ƙaunace mu, har ya ba da kansa dominmu a matsayin sadaka mai ƙanshi da kuma hadaya ga Allah.
y vivid en amor así como Cristo os amó, y se entregó por nosotros como oblación y víctima a Dios cual ( incienso de ) olor suavísimo.
3 Kada a ma ambaci fasikanci, da kowane irin aikin lalata, ko kwaɗayi a tsakaninku, domin bai dace da mutane masu tsarki na Allah ba.
Fornicación y cualquier impureza o avaricia, ni siquiera se nombre entre vosotros, como conviene a santos;
4 Haka ma bai kamata a sami datti, ƙazamar magana, ko zancen banza a cikinku ba, domin ba su dace ba, a maimakon haka sai ku yi ta yin godiya.
ni torpeza, ni vana palabrería, ni bufonerías, cosas que no convienen, antes bien acciones de gracia.
5 Ku dai tabbata, ba wani mai fasikanci, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayin (wanda shi da mai bautar gumaka ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Kiristi da na Allah.
Porque tened bien entendido que ningún fornicario, impuro o avaro, que es lo mismo que idólatra, tiene parte en el reino de Cristo y de Dios.
6 Kada wani yă ruɗe ku da kalmomin wofi, gama saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake zuwa a kan marasa biyayya.
Nadie os engañe con vanas palabras, pues por estas cosas descarga la ira de Dios sobre los hijos de la desobediencia.
7 Saboda haka kada ku haɗa kai da su.
No os hagáis, pues, copartícipes de ellos.
8 Gama a dā zukatanku sun cika da duhu, amma yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi rayuwa kamar’ya’yan haske
Porque antes erais tinieblas, ahora sois luz en el Señor. Andad, pues, como hijos de la luz —
9 (domin amfanin haske ya ƙunshi nagarta, adalci, da kuma gaskiya)
el fruto de la luz consiste en toda bondad y justicia y verdad—
10 ku nemi abin da zai gamshi Ubangiji.
aprendiendo por experiencia que es lo que agrada al Señor;
11 Ku yi nesa da ayyukan duhun da mutane suke yi, a maimakon haka, ku tona su.
y no toméis parte con ellos en las obras infructuosas de las tinieblas, antes bien manifestad abiertamente vuestra reprobación;
12 Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da marasa biyayya suke yi a ɓoye.
porque si bien da vergüenza hasta el nombrar las cosas que ellos hacen en secreto,
13 Duk abin da aka kawo a gaban haske ana iya ganinsa, kuma duk abin da aka haskaka yakan zama haske.
sin embargo todas las cosas, una vez condenadas, son descubiertas por la luz, y todo lo que es manifiesto es luz.
14 Shi ya sa aka ce, “Ka farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu, Kiristi kuwa zai haskaka ka.”
Por eso dice: “Despierta tú que duermes, y levántate de entre los muertos, y Cristo te iluminará”.
15 Sai ku yi hankali sosai da yadda kuke rayuwa, kada ku zama kamar marasa hikima, sai dai kamar masu hikima.
Mirad, pues, con gran cautela cómo andáis; no como necios, sino como sabios,
16 Ku kuma yi matuƙar amfani da kowane zarafi, don kwanakin nan mugaye ne.
aprovechando bien el tiempo, porque los días son malos.
17 Saboda haka kada ku zama wawaye, sai dai ku fahimci ko mene ne nufin Ubangiji.
Por lo tanto, no os hagáis los desentendidos, sino entended cuál sea la voluntad del Señor.
18 Kada ku bugu da ruwan inabi, wanda yake kai ga lalaci. A maimako haka, ku cika da Ruhu.
Y no os embriaguéis con vino, en el cual hay lujuria, sino llenaos en el Espíritu,
19 Ku yi zance da juna cikin zabura, da waƙoƙi, da kuma waƙoƙin ruhaniya. Ku rera, ku kuma yi kiɗe-kiɗe a zuciyarku ga Ubangiji.
entreteniéndoos entre vosotros con salmos, himnos y cánticos espirituales, cantando y alabando de todo corazón al Señor,
20 Kullum ku dinga yin amfani da sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, kuna gode wa Allah Uba a kome.
dando gracias siempre y por todo al Dios y Padre en el nombre de nuestro Señor Jesucristo,
21 Ku yi biyayya da juna saboda bangirmar da kuke nuna wa Kiristi.
sujetándoos los unos a los otros en el santo temor de Cristo.
22 Matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, kamar ga Ubangiji ne kuke yi.
Las mujeres sujétense a sus maridos como al Señor,
23 Gama miji shi ne kan mace, yadda Kiristi yake kai da kuma Mai Ceton ikkilisiya, wadda take jikinsa.
porque el varón es cabeza de la mujer, como Cristo cabeza de la Iglesia, salvador de su cuerpo.
24 To, kamar yadda ikkilisiya take biyayya ga Kiristi, haka ma ya kamata mata su yi biyayya ga mazansu cikin kome.
Así como la Iglesia está sujeta a Cristo, así también las mujeres lo han de estar a sus maridos en todo.
25 Maza, ku ƙaunaci matanku, kamar yadda Kiristi ya ƙaunaci ikkilisiya, ya kuma ba da kansa dominta.
Maridos, amad a vuestras mujeres, como Cristo amó a la Iglesia y se entregó Él mismo por ella,
26 Ya mai da ikkilisiya ta zama mai tsarki ta wurin ikon maganarsa, ya kuma tsabtacce ta ta wurin wanke ta da ruwa.
para santificarla, purificándola con la palabra en el baño del agua,
27 Kiristi ya yi haka don yă miƙa wa kansa ikkilisiya mai ɗaukaka da kuma mai tsarki, marar aibi, marar tabo, da kuma marar lahani.
a fin de presentarla delante de Sí mismo como Iglesia gloriosa, sin mancha, ni arruga, ni nada semejante, sino santa e inmaculada.
28 Don haka, dole maza su ƙaunaci matansu kamar yadda suke ƙaunar jikunansu. Wanda yake ƙaunar matarsa, yana ƙaunar kansa ne.
Así también los varones deben amar a sus mujeres como a su propio cuerpo. El que ama a su mujer, a sí mismo se ama.
29 Gama ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai yă ciyar da shi, yă kuma kula da shi, kamar yadda Kiristi yake yi wa ikkilisiya,
Porque nadie jamás tuvo odio a su propia carne, sino que la sustenta y regala, como también Cristo a la Iglesia,
30 gama mu gaɓoɓin jikinsa ne.
puesto que somos miembros de su cuerpo.
31 “Saboda haka mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su biyun su zama jiki ɗaya.”
“A causa de esto dejará el hombre a su padre y a su madre, y se adherirá a su mujer, y los dos serán una carne”.
32 Wannan babban asiri ne, amma na ɗauke shi a matsayin kwatanci ne na Kiristi da ikkilisiya.
Este misterio es grande; mas yo lo digo en orden a Cristo y a la Iglesia.
33 Duk da haka, dole kowannenku yă ƙaunaci matarsa kamar yadda yake ƙaunar kansa, kuma dole matar tă yi biyayya ga mijinta.
Con todo, también cada uno de vosotros ame a su mujer como a sí mismo; y la mujer a su vez reverencie al marido.

< Afisawa 5 >