< Afisawa 5 >

1 Ku zama masu koyi da Allah, kamar ƙaunatattun’ya’ya,
atO yUyaM priyabAlakA ivEzvarasyAnukAriNO bhavata,
2 ku kuma yi rayuwar ƙauna, kamar yadda Kiristi ya ƙaunace mu, har ya ba da kansa dominmu a matsayin sadaka mai ƙanshi da kuma hadaya ga Allah.
khrISTa iva prEmAcAraM kuruta ca, yataH sO'smAsu prEma kRtavAn asmAkaM vinimayEna cAtmanivEdanaM kRtvA grAhyasugandhArthakam upahAraM balinjcEzvarAca dattavAn|
3 Kada a ma ambaci fasikanci, da kowane irin aikin lalata, ko kwaɗayi a tsakaninku, domin bai dace da mutane masu tsarki na Allah ba.
kintu vEzyAgamanaM sarvvavidhAzaucakriyA lObhazcaitESAm uccAraNamapi yuSmAkaM madhyE na bhavatu, EtadEva pavitralOkAnAm ucitaM|
4 Haka ma bai kamata a sami datti, ƙazamar magana, ko zancen banza a cikinku ba, domin ba su dace ba, a maimakon haka sai ku yi ta yin godiya.
aparaM kutsitAlApaH pralApaH zlESOktizca na bhavatu yata EtAnyanucitAni kintvIzvarasya dhanyavAdO bhavatu|
5 Ku dai tabbata, ba wani mai fasikanci, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayin (wanda shi da mai bautar gumaka ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Kiristi da na Allah.
vEzyAgAmyazaucAcArI dEvapUjaka iva gaNyO lObhI caitESAM kOSi khrISTasya rAjyE'rthata Izvarasya rAjyE kamapyadhikAraM na prApsyatIti yuSmAbhiH samyak jnjAyatAM|
6 Kada wani yă ruɗe ku da kalmomin wofi, gama saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake zuwa a kan marasa biyayya.
anarthakavAkyEna kO'pi yuSmAn na vanjcayatu yatastAdRgAcArahEtOranAjnjAgrAhiSu lOkESvIzvarasya kOpO varttatE|
7 Saboda haka kada ku haɗa kai da su.
tasmAd yUyaM taiH sahabhAginO na bhavata|
8 Gama a dā zukatanku sun cika da duhu, amma yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi rayuwa kamar’ya’yan haske
pUrvvaM yUyam andhakArasvarUpA AdhvaM kintvidAnIM prabhunA dIptisvarUpA bhavatha tasmAd dIptEH santAnA iva samAcarata|
9 (domin amfanin haske ya ƙunshi nagarta, adalci, da kuma gaskiya)
dIptE ryat phalaM tat sarvvavidhahitaiSitAyAM dharmmE satyAlApE ca prakAzatE|
10 ku nemi abin da zai gamshi Ubangiji.
prabhavE yad rOcatE tat parIkSadhvaM|
11 Ku yi nesa da ayyukan duhun da mutane suke yi, a maimakon haka, ku tona su.
yUyaM timirasya viphalakarmmaNAm aMzinO na bhUtvA tESAM dOSitvaM prakAzayata|
12 Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da marasa biyayya suke yi a ɓoye.
yatastE lOkA rahami yad yad Acaranti taduccAraNam api lajjAjanakaM|
13 Duk abin da aka kawo a gaban haske ana iya ganinsa, kuma duk abin da aka haskaka yakan zama haske.
yatO dIptyA yad yat prakAzyatE tat tayA cakAsyatE yacca cakAsti tad dIptisvarUpaM bhavati|
14 Shi ya sa aka ce, “Ka farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu, Kiristi kuwa zai haskaka ka.”
EtatkAraNAd uktam AstE, "hE nidrita prabudhyasva mRtEbhyazcOtthitiM kuru| tatkRtE sUryyavat khrISTaH svayaM tvAM dyOtayiSyati|"
15 Sai ku yi hankali sosai da yadda kuke rayuwa, kada ku zama kamar marasa hikima, sai dai kamar masu hikima.
ataH sAvadhAnA bhavata, ajnjAnA iva mAcarata kintu jnjAnina iva satarkam Acarata|
16 Ku kuma yi matuƙar amfani da kowane zarafi, don kwanakin nan mugaye ne.
samayaM bahumUlyaM gaNayadhvaM yataH kAlA abhadrAH|
17 Saboda haka kada ku zama wawaye, sai dai ku fahimci ko mene ne nufin Ubangiji.
tasmAd yUyam ajnjAnA na bhavata kintu prabhOrabhimataM kiM tadavagatA bhavata|
18 Kada ku bugu da ruwan inabi, wanda yake kai ga lalaci. A maimako haka, ku cika da Ruhu.
sarvvanAzajanakEna surApAnEna mattA mA bhavata kintvAtmanA pUryyadhvaM|
19 Ku yi zance da juna cikin zabura, da waƙoƙi, da kuma waƙoƙin ruhaniya. Ku rera, ku kuma yi kiɗe-kiɗe a zuciyarku ga Ubangiji.
aparaM gItai rgAnaiH pAramArthikakIrttanaizca parasparam AlapantO manasA sArddhaM prabhum uddizya gAyata vAdayata ca|
20 Kullum ku dinga yin amfani da sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, kuna gode wa Allah Uba a kome.
sarvvadA sarvvaviSayE'smatprabhO yIzOH khrISTasya nAmnA tAtam IzvaraM dhanyaM vadata|
21 Ku yi biyayya da juna saboda bangirmar da kuke nuna wa Kiristi.
yUyam IzvarAd bhItAH santa anyE'parESAM vazIbhUtA bhavata|
22 Matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, kamar ga Ubangiji ne kuke yi.
hE yOSitaH, yUyaM yathA prabhOstathA svasvasvAminO vazaggatA bhavata|
23 Gama miji shi ne kan mace, yadda Kiristi yake kai da kuma Mai Ceton ikkilisiya, wadda take jikinsa.
yataH khrISTO yadvat samitE rmUrddhA zarIrasya trAtA ca bhavati tadvat svAmI yOSitO mUrddhA|
24 To, kamar yadda ikkilisiya take biyayya ga Kiristi, haka ma ya kamata mata su yi biyayya ga mazansu cikin kome.
ataH samiti ryadvat khrISTasya vazIbhUtA tadvad yOSidbhirapi svasvasvAminO vazatA svIkarttavyA|
25 Maza, ku ƙaunaci matanku, kamar yadda Kiristi ya ƙaunaci ikkilisiya, ya kuma ba da kansa dominta.
aparanjca hE puruSAH, yUyaM khrISTa iva svasvayOSitsu prIyadhvaM|
26 Ya mai da ikkilisiya ta zama mai tsarki ta wurin ikon maganarsa, ya kuma tsabtacce ta ta wurin wanke ta da ruwa.
sa khrISTO'pi samitau prItavAn tasyAH kRtE ca svaprANAn tyaktavAn yataH sa vAkyE jalamajjanEna tAM pariSkRtya pAvayitum
27 Kiristi ya yi haka don yă miƙa wa kansa ikkilisiya mai ɗaukaka da kuma mai tsarki, marar aibi, marar tabo, da kuma marar lahani.
aparaM tilakavalyAdivihInAM pavitrAM niSkalagkAnjca tAM samitiM tEjasvinIM kRtvA svahastE samarpayitunjcAbhilaSitavAn|
28 Don haka, dole maza su ƙaunaci matansu kamar yadda suke ƙaunar jikunansu. Wanda yake ƙaunar matarsa, yana ƙaunar kansa ne.
tasmAt svatanuvat svayOSiti prEmakaraNaM puruSasyOcitaM, yEna svayOSiti prEma kriyatE tEnAtmaprEma kriyatE|
29 Gama ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai yă ciyar da shi, yă kuma kula da shi, kamar yadda Kiristi yake yi wa ikkilisiya,
kO'pi kadApi na svakIyAM tanum RtIyitavAn kintu sarvvE tAM vibhrati puSNanti ca| khrISTO'pi samitiM prati tadEva karOti,
30 gama mu gaɓoɓin jikinsa ne.
yatO vayaM tasya zarIrasyAggAni mAMsAsthIni ca bhavAmaH|
31 “Saboda haka mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su biyun su zama jiki ɗaya.”
EtadarthaM mAnavaH svamAtApitarO parityajya svabhAryyAyAm AsaMkSyati tau dvau janAvEkAggau bhaviSyataH|
32 Wannan babban asiri ne, amma na ɗauke shi a matsayin kwatanci ne na Kiristi da ikkilisiya.
EtannigUPhavAkyaM gurutaraM mayA ca khrISTasamitI adhi tad ucyatE|
33 Duk da haka, dole kowannenku yă ƙaunaci matarsa kamar yadda yake ƙaunar kansa, kuma dole matar tă yi biyayya ga mijinta.
ataEva yuSmAkam EkaikO jana Atmavat svayOSiti prIyatAM bhAryyApi svAminaM samAdarttuM yatatAM|

< Afisawa 5 >