< Afisawa 5 >

1 Ku zama masu koyi da Allah, kamar ƙaunatattun’ya’ya,
Therefore imitate God, as his dear children,
2 ku kuma yi rayuwar ƙauna, kamar yadda Kiristi ya ƙaunace mu, har ya ba da kansa dominmu a matsayin sadaka mai ƙanshi da kuma hadaya ga Allah.
and live a life of love, following the example of the Christ, who loved you and gave himself for you as ‘an offering and a sacrifice to God, that should be fragrant and acceptable.’
3 Kada a ma ambaci fasikanci, da kowane irin aikin lalata, ko kwaɗayi a tsakaninku, domin bai dace da mutane masu tsarki na Allah ba.
As for unchastity and every kind of impurity, or greed, do not let them even be mentioned among you, as befits Christ’s People,
4 Haka ma bai kamata a sami datti, ƙazamar magana, ko zancen banza a cikinku ba, domin ba su dace ba, a maimakon haka sai ku yi ta yin godiya.
nor shameful conduct, nor foolish talk or jesting, for they are wholly out of place among you; but rather thanksgiving.
5 Ku dai tabbata, ba wani mai fasikanci, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayin (wanda shi da mai bautar gumaka ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Kiristi da na Allah.
For of this you may be sure — that no one who is unchaste or impure or greedy of gain (for to be greedy of gain is idolatry) has any place awaiting him in the kingdom of the Christ and God.
6 Kada wani yă ruɗe ku da kalmomin wofi, gama saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake zuwa a kan marasa biyayya.
Do not let any one deceive you with specious arguments. Those are the sins that bring down the Wrath of God upon the disobedient.
7 Saboda haka kada ku haɗa kai da su.
Therefore have nothing to do with such people.
8 Gama a dā zukatanku sun cika da duhu, amma yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi rayuwa kamar’ya’yan haske
For, although you were once in Darkness, now, by your union with the Lord, you are in the Light. Live as ‘Children of Light’ —
9 (domin amfanin haske ya ƙunshi nagarta, adalci, da kuma gaskiya)
For the outcome of life in the Light may be seen in every form of goodness, righteousness, and sincerity —
10 ku nemi abin da zai gamshi Ubangiji.
Always trying to find out what is pleasing to the Lord.
11 Ku yi nesa da ayyukan duhun da mutane suke yi, a maimakon haka, ku tona su.
Take no part in deeds of Darkness, from which no good can come; on the contrary, expose them.
12 Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da marasa biyayya suke yi a ɓoye.
It is degrading even to speak of the things continually done by them in secret.
13 Duk abin da aka kawo a gaban haske ana iya ganinsa, kuma duk abin da aka haskaka yakan zama haske.
All such actions, when exposed, have their true character made manifest by the Light.
14 Shi ya sa aka ce, “Ka farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu, Kiristi kuwa zai haskaka ka.”
For everything that has its true character made manifest is clear as light. And that is why it is said — ‘Sleeper, awake! Arise from the dead, And the Christ shall give thee light!’
15 Sai ku yi hankali sosai da yadda kuke rayuwa, kada ku zama kamar marasa hikima, sai dai kamar masu hikima.
Take great care, then, how you live — not unwisely but wisely,
16 Ku kuma yi matuƙar amfani da kowane zarafi, don kwanakin nan mugaye ne.
making the most of every opportunity; for these are evil days.
17 Saboda haka kada ku zama wawaye, sai dai ku fahimci ko mene ne nufin Ubangiji.
Therefore do not grow thoughtless, but try to understand what the Lord’s will is.
18 Kada ku bugu da ruwan inabi, wanda yake kai ga lalaci. A maimako haka, ku cika da Ruhu.
Do not drink wine to excess, for that leads to profligacy; but seek to be filled with the Spirit of God, and speak to one another in psalms and hymns and sacred songs.
19 Ku yi zance da juna cikin zabura, da waƙoƙi, da kuma waƙoƙin ruhaniya. Ku rera, ku kuma yi kiɗe-kiɗe a zuciyarku ga Ubangiji.
Sing and make music in your hearts to the Lord.
20 Kullum ku dinga yin amfani da sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, kuna gode wa Allah Uba a kome.
Always give thanks for everything to our God and Father, in the Name of our Lord Jesus Christ;
21 Ku yi biyayya da juna saboda bangirmar da kuke nuna wa Kiristi.
and submit to one another from reverence for him.
22 Matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, kamar ga Ubangiji ne kuke yi.
Wives should submit to their husbands as submitting to the Lord.
23 Gama miji shi ne kan mace, yadda Kiristi yake kai da kuma Mai Ceton ikkilisiya, wadda take jikinsa.
For a man is the Head of his wife, as the Christ is the Head of the Church — being indeed himself the Saviour of his Body.
24 To, kamar yadda ikkilisiya take biyayya ga Kiristi, haka ma ya kamata mata su yi biyayya ga mazansu cikin kome.
But as the Church submits to the Christ, so also should wives submit to their husbands in everything.
25 Maza, ku ƙaunaci matanku, kamar yadda Kiristi ya ƙaunaci ikkilisiya, ya kuma ba da kansa dominta.
Husbands, love your wives, just as the Christ loved the Church, and gave himself for her,
26 Ya mai da ikkilisiya ta zama mai tsarki ta wurin ikon maganarsa, ya kuma tsabtacce ta ta wurin wanke ta da ruwa.
to make her holy, after purifying her by the Washing with the Water, according to his promise;
27 Kiristi ya yi haka don yă miƙa wa kansa ikkilisiya mai ɗaukaka da kuma mai tsarki, marar aibi, marar tabo, da kuma marar lahani.
so that he might himself bring the Church, in all her beauty, into his own presence, with no spot or wrinkle or blemish of any kind, but that she might be holy and faultless.
28 Don haka, dole maza su ƙaunaci matansu kamar yadda suke ƙaunar jikunansu. Wanda yake ƙaunar matarsa, yana ƙaunar kansa ne.
That is how husbands ought to love their wives — as if they were their own bodies. A man who loves his wife is really loving himself;
29 Gama ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai yă ciyar da shi, yă kuma kula da shi, kamar yadda Kiristi yake yi wa ikkilisiya,
for no one ever yet hated his own body. But every one feeds his body and cares for it, just as the Christ for the Church;
30 gama mu gaɓoɓin jikinsa ne.
for we are members of his Body.
31 “Saboda haka mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su biyun su zama jiki ɗaya.”
‘For this cause a man shall leave his father and mother, and be united to his wife; and the man and his wife shall become one.’
32 Wannan babban asiri ne, amma na ɗauke shi a matsayin kwatanci ne na Kiristi da ikkilisiya.
In this there is a profound truth — I am speaking of Christ and his Church.
33 Duk da haka, dole kowannenku yă ƙaunaci matarsa kamar yadda yake ƙaunar kansa, kuma dole matar tă yi biyayya ga mijinta.
However, for you individually, let each love his wife as if she were himself; and the wife be careful to respect her husband.

< Afisawa 5 >