< Afisawa 5 >

1 Ku zama masu koyi da Allah, kamar ƙaunatattun’ya’ya,
Become ye, therefore, imitators of God, as children beloved,
2 ku kuma yi rayuwar ƙauna, kamar yadda Kiristi ya ƙaunace mu, har ya ba da kansa dominmu a matsayin sadaka mai ƙanshi da kuma hadaya ga Allah.
And walk in love—even as, the Christ also, loved you, and delivered himself up in your behalf, an offering and sacrifice unto God, for a fragrance of sweet smell.
3 Kada a ma ambaci fasikanci, da kowane irin aikin lalata, ko kwaɗayi a tsakaninku, domin bai dace da mutane masu tsarki na Allah ba.
But, fornication, and all impurity, or covetousness, let it not be named among you—even as becometh saints;
4 Haka ma bai kamata a sami datti, ƙazamar magana, ko zancen banza a cikinku ba, domin ba su dace ba, a maimakon haka sai ku yi ta yin godiya.
And shamelessness and foolish talking, or jesting, —which things are beneath you, —but, rather, giving of thanks;
5 Ku dai tabbata, ba wani mai fasikanci, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayin (wanda shi da mai bautar gumaka ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Kiristi da na Allah.
For, this, ye know, if ye take note—that no fornicator, or impure or greedy person, who is an idolater, hath any inheritance in the kingdom of the Christ and God.
6 Kada wani yă ruɗe ku da kalmomin wofi, gama saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake zuwa a kan marasa biyayya.
Let no one be deceiving you with empty words; for, because of these things, is coming the anger of God upon the sons of obstinacy:
7 Saboda haka kada ku haɗa kai da su.
Do not, then, become co-partners with them;
8 Gama a dā zukatanku sun cika da duhu, amma yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi rayuwa kamar’ya’yan haske
For ye were, at one time, darkness, but, now, are ye light in the Lord, —as children of light, be walking,
9 (domin amfanin haske ya ƙunshi nagarta, adalci, da kuma gaskiya)
For, the fruit of the light, is in all goodness, and righteousness, and truth, —
10 ku nemi abin da zai gamshi Ubangiji.
Putting to the test what is well-pleasing unto the Lord;
11 Ku yi nesa da ayyukan duhun da mutane suke yi, a maimakon haka, ku tona su.
And be not joining in fellowship in the unfruitful works of darkness, but, rather, be even administering reproof;
12 Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da marasa biyayya suke yi a ɓoye.
For, of the secret things which are brought to pass by them, it is, shameful, even to speak!
13 Duk abin da aka kawo a gaban haske ana iya ganinsa, kuma duk abin da aka haskaka yakan zama haske.
All things, however, when reproved by the light, become manifest, for, all that of itself maketh manifest, is, light;
14 Shi ya sa aka ce, “Ka farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu, Kiristi kuwa zai haskaka ka.”
Wherefore it saith—Up! thou sleeper, and arise from among the dead, and the Christ will shine upon thee.
15 Sai ku yi hankali sosai da yadda kuke rayuwa, kada ku zama kamar marasa hikima, sai dai kamar masu hikima.
Be taking heed, therefore, exactly how ye are walking, —not as unwise, but as wise, —
16 Ku kuma yi matuƙar amfani da kowane zarafi, don kwanakin nan mugaye ne.
Buying out for yourselves the opportunity, because, the days, are evil;
17 Saboda haka kada ku zama wawaye, sai dai ku fahimci ko mene ne nufin Ubangiji.
For this cause, do not become foolish, but have discernment as to what is the will of the Lord;
18 Kada ku bugu da ruwan inabi, wanda yake kai ga lalaci. A maimako haka, ku cika da Ruhu.
And be not getting drunk with wine, in which is dissoluteness, but be getting filled in Spirit; —
19 Ku yi zance da juna cikin zabura, da waƙoƙi, da kuma waƙoƙin ruhaniya. Ku rera, ku kuma yi kiɗe-kiɗe a zuciyarku ga Ubangiji.
Speaking to yourselves, with psalms and hymns and spiritual songs; singing, and striking the strings, with your heart unto the Lord;
20 Kullum ku dinga yin amfani da sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, kuna gode wa Allah Uba a kome.
Giving thanks, always, for all things, in the name of our Lord Jesus Christ, unto your God and Father;
21 Ku yi biyayya da juna saboda bangirmar da kuke nuna wa Kiristi.
Submitting yourselves one to another in reverence of Christ, —
22 Matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, kamar ga Ubangiji ne kuke yi.
Ye wives, unto your own husbands, as unto the Lord,
23 Gama miji shi ne kan mace, yadda Kiristi yake kai da kuma Mai Ceton ikkilisiya, wadda take jikinsa.
Because, a husband, is the head of his wife, as, the Christ also, is the head of the assembly, he, being the saviour of the body, —
24 To, kamar yadda ikkilisiya take biyayya ga Kiristi, haka ma ya kamata mata su yi biyayya ga mazansu cikin kome.
Nevertheless, as, the assembly, submitteth herself unto the Christ, so, the wives, unto their husbands, in everything:
25 Maza, ku ƙaunaci matanku, kamar yadda Kiristi ya ƙaunaci ikkilisiya, ya kuma ba da kansa dominta.
Ye husbands, be loving your wives, even as, the Christ also, loved the assembly, and delivered, himself, up in her behalf,
26 Ya mai da ikkilisiya ta zama mai tsarki ta wurin ikon maganarsa, ya kuma tsabtacce ta ta wurin wanke ta da ruwa.
That, her, he might sanctify, having purified [her] with the bath of water, in declaration,
27 Kiristi ya yi haka don yă miƙa wa kansa ikkilisiya mai ɗaukaka da kuma mai tsarki, marar aibi, marar tabo, da kuma marar lahani.
That, he, might present, unto himself, the assembly, all glorious, not having spot or wrinkle or any of such things, but that she should be holy and blameless;
28 Don haka, dole maza su ƙaunaci matansu kamar yadda suke ƙaunar jikunansu. Wanda yake ƙaunar matarsa, yana ƙaunar kansa ne.
So, ought the husbands [also] to be loving their own wives, as their own bodies, —he that loveth his own wife, loveth himself,
29 Gama ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai yă ciyar da shi, yă kuma kula da shi, kamar yadda Kiristi yake yi wa ikkilisiya,
No one, in fact, ever yet hated, his own flesh, but nourisheth and cherisheth it, —even as, the Christ, the assembly,
30 gama mu gaɓoɓin jikinsa ne.
Because, members, are we of his body; —
31 “Saboda haka mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su biyun su zama jiki ɗaya.”
For this cause, will a man leave his father and his mother, and will cleave unto his wife, and, they two, shall become, one flesh.
32 Wannan babban asiri ne, amma na ɗauke shi a matsayin kwatanci ne na Kiristi da ikkilisiya.
This sacred secret, is, great, —I, however, am speaking as to Christ and [as to] the assembly; —
33 Duk da haka, dole kowannenku yă ƙaunaci matarsa kamar yadda yake ƙaunar kansa, kuma dole matar tă yi biyayya ga mijinta.
Nevertheless, ye also, do ye, individually, each man be so loving, his own wife, as himself, and, the wife, [see] that she reverence her husband.

< Afisawa 5 >