< Afisawa 5 >
1 Ku zama masu koyi da Allah, kamar ƙaunatattun’ya’ya,
Be therefore imitators of God, as beloved children;
2 ku kuma yi rayuwar ƙauna, kamar yadda Kiristi ya ƙaunace mu, har ya ba da kansa dominmu a matsayin sadaka mai ƙanshi da kuma hadaya ga Allah.
and walk in love, as Christ also loved you, and gave himself for you an offering and a sacrifice to God, of a sweet odor.
3 Kada a ma ambaci fasikanci, da kowane irin aikin lalata, ko kwaɗayi a tsakaninku, domin bai dace da mutane masu tsarki na Allah ba.
But fornication, and all uncleanness, or covetousness, let it not even be named among you, as becometh saints,
4 Haka ma bai kamata a sami datti, ƙazamar magana, ko zancen banza a cikinku ba, domin ba su dace ba, a maimakon haka sai ku yi ta yin godiya.
neither obscenity, nor foolish talking, nor indecent jesting, which are not becoming; but rather giving of thanks.
5 Ku dai tabbata, ba wani mai fasikanci, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayin (wanda shi da mai bautar gumaka ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Kiristi da na Allah.
For of this ye are sure, since ye know that no whore-monger, nor unclean person, nor covetous man, who is an idolater, hath an inheritance in the kingdom of Christ and God.
6 Kada wani yă ruɗe ku da kalmomin wofi, gama saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake zuwa a kan marasa biyayya.
Let no one deceive you with vain words; for because of these things the wrath of God cometh upon the sons of disobedience.
7 Saboda haka kada ku haɗa kai da su.
Be not therefore partakers with them.
8 Gama a dā zukatanku sun cika da duhu, amma yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi rayuwa kamar’ya’yan haske
For ye were once darkness, but now ye are light in the Lord. Walk as children of light,
9 (domin amfanin haske ya ƙunshi nagarta, adalci, da kuma gaskiya)
—for the fruit of the light is in all goodness, and righteousness, and truth, —
10 ku nemi abin da zai gamshi Ubangiji.
proving what is acceptable to the Lord;
11 Ku yi nesa da ayyukan duhun da mutane suke yi, a maimakon haka, ku tona su.
and have no fellowship with the unfruitful works of darkness, but rather even reprove them.
12 Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da marasa biyayya suke yi a ɓoye.
For the things done in secret by them it is a shame even to speak of.
13 Duk abin da aka kawo a gaban haske ana iya ganinsa, kuma duk abin da aka haskaka yakan zama haske.
But all things, when reproved, are made manifest by the light; for whatever maketh manifest is light.
14 Shi ya sa aka ce, “Ka farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu, Kiristi kuwa zai haskaka ka.”
Wherefore he saith, “Awake, thou that sleepest, and arise from the dead, and Christ will give thee light.”
15 Sai ku yi hankali sosai da yadda kuke rayuwa, kada ku zama kamar marasa hikima, sai dai kamar masu hikima.
See then that ye walk circumspectly; not as unwise men, but as wise;
16 Ku kuma yi matuƙar amfani da kowane zarafi, don kwanakin nan mugaye ne.
buying up for yourselves opportunities, because the days are evil.
17 Saboda haka kada ku zama wawaye, sai dai ku fahimci ko mene ne nufin Ubangiji.
Wherefore be not unwise, but understanding what the will of the Lord is.
18 Kada ku bugu da ruwan inabi, wanda yake kai ga lalaci. A maimako haka, ku cika da Ruhu.
And be not drunk with wine, in which is dissoluteness, but be filled with the Spirit,
19 Ku yi zance da juna cikin zabura, da waƙoƙi, da kuma waƙoƙin ruhaniya. Ku rera, ku kuma yi kiɗe-kiɗe a zuciyarku ga Ubangiji.
speaking to one another in psalms, and hymns, and spiritual songs, singing and making melody in your heart to the Lord;
20 Kullum ku dinga yin amfani da sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, kuna gode wa Allah Uba a kome.
giving thanks always for all things to God, the Father, in the name of our Lord Jesus Christ,
21 Ku yi biyayya da juna saboda bangirmar da kuke nuna wa Kiristi.
submitting yourselves one to another in the fear of Christ.
22 Matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, kamar ga Ubangiji ne kuke yi.
Wives, submit yourselves to your own husbands, as to the Lord;
23 Gama miji shi ne kan mace, yadda Kiristi yake kai da kuma Mai Ceton ikkilisiya, wadda take jikinsa.
for the husband is the head of the wife, even as Christ is the head of the church, —he, who is the Saviour of the body.
24 To, kamar yadda ikkilisiya take biyayya ga Kiristi, haka ma ya kamata mata su yi biyayya ga mazansu cikin kome.
But as the church is subject to Christ, so let wives be to their husbands in everything.
25 Maza, ku ƙaunaci matanku, kamar yadda Kiristi ya ƙaunaci ikkilisiya, ya kuma ba da kansa dominta.
Husbands, love your wives, as Christ also loved the church, and gave himself up for it,
26 Ya mai da ikkilisiya ta zama mai tsarki ta wurin ikon maganarsa, ya kuma tsabtacce ta ta wurin wanke ta da ruwa.
that he might sanctify it, having cleansed it by the bath of the water in the word;
27 Kiristi ya yi haka don yă miƙa wa kansa ikkilisiya mai ɗaukaka da kuma mai tsarki, marar aibi, marar tabo, da kuma marar lahani.
that he himself might present to himself the church, glorious, having no spot or wrinkle, or any such thing, but that it should be holy and without blemish.
28 Don haka, dole maza su ƙaunaci matansu kamar yadda suke ƙaunar jikunansu. Wanda yake ƙaunar matarsa, yana ƙaunar kansa ne.
In like manner husbands ought to love their own wives as their own bodies. He that loveth his own wife loveth himself;
29 Gama ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai yă ciyar da shi, yă kuma kula da shi, kamar yadda Kiristi yake yi wa ikkilisiya,
for no one ever yet hated his own flesh, but nourisheth and cherisheth it, even as Christ doth the church;
30 gama mu gaɓoɓin jikinsa ne.
for we are members of his body, of his flesh, and of his bones.
31 “Saboda haka mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su biyun su zama jiki ɗaya.”
“For this cause shall a man leave father and mother, and shall cleave to his wife, and they two shall be one flesh.”
32 Wannan babban asiri ne, amma na ɗauke shi a matsayin kwatanci ne na Kiristi da ikkilisiya.
This mystery is a great one; but I am speaking of Christ and of the church.
33 Duk da haka, dole kowannenku yă ƙaunaci matarsa kamar yadda yake ƙaunar kansa, kuma dole matar tă yi biyayya ga mijinta.
However, do ye also severally love each one his own wife as himself; and let the wife see that she reverence her husband.