< Afisawa 5 >
1 Ku zama masu koyi da Allah, kamar ƙaunatattun’ya’ya,
Be therefore imitators of God, as beloved children.
2 ku kuma yi rayuwar ƙauna, kamar yadda Kiristi ya ƙaunace mu, har ya ba da kansa dominmu a matsayin sadaka mai ƙanshi da kuma hadaya ga Allah.
And walk in love, even as Meshikha also loved us, and gave himself up for us, an offering and a sacrifice to God for a sweet-smelling fragrance.
3 Kada a ma ambaci fasikanci, da kowane irin aikin lalata, ko kwaɗayi a tsakaninku, domin bai dace da mutane masu tsarki na Allah ba.
But sexual immorality, and all uncleanness, or covetousness, let it not even be mentioned among you, as becomes saints;
4 Haka ma bai kamata a sami datti, ƙazamar magana, ko zancen banza a cikinku ba, domin ba su dace ba, a maimakon haka sai ku yi ta yin godiya.
nor filthiness, nor foolish talking, nor jesting, which are not appropriate; but rather giving of thanks.
5 Ku dai tabbata, ba wani mai fasikanci, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayin (wanda shi da mai bautar gumaka ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Kiristi da na Allah.
Know this for sure, that no sexually immoral or impure or greedy person, that is, an idolater, has any inheritance in the Kingdom of Meshikha and God.
6 Kada wani yă ruɗe ku da kalmomin wofi, gama saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake zuwa a kan marasa biyayya.
Let no one deceive you with empty words. For because of these things, the wrath of God comes on the children of disobedience.
7 Saboda haka kada ku haɗa kai da su.
Therefore do not be partakers with them.
8 Gama a dā zukatanku sun cika da duhu, amma yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi rayuwa kamar’ya’yan haske
For you were once darkness, but are now light in the Lord. Walk as children of light,
9 (domin amfanin haske ya ƙunshi nagarta, adalci, da kuma gaskiya)
for the fruit of the light is in all goodness and righteousness and truth,
10 ku nemi abin da zai gamshi Ubangiji.
proving what is well pleasing to the Lord.
11 Ku yi nesa da ayyukan duhun da mutane suke yi, a maimakon haka, ku tona su.
Have no fellowship with the unfruitful works of darkness, but rather even reprove them.
12 Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da marasa biyayya suke yi a ɓoye.
For the things which are done by them in secret, it is a shame even to speak of.
13 Duk abin da aka kawo a gaban haske ana iya ganinsa, kuma duk abin da aka haskaka yakan zama haske.
But all things, when they are reproved, are revealed by the light, for everything that reveals is light.
14 Shi ya sa aka ce, “Ka farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu, Kiristi kuwa zai haskaka ka.”
Therefore he says, "Awake, you who sleep, and rise from the dead, and Meshikha will shine on you."
15 Sai ku yi hankali sosai da yadda kuke rayuwa, kada ku zama kamar marasa hikima, sai dai kamar masu hikima.
Therefore watch carefully how you walk, not as unwise, but as wise;
16 Ku kuma yi matuƙar amfani da kowane zarafi, don kwanakin nan mugaye ne.
redeeming the time, because the days are evil.
17 Saboda haka kada ku zama wawaye, sai dai ku fahimci ko mene ne nufin Ubangiji.
Therefore do not be foolish, but understand what the will of the Lord is.
18 Kada ku bugu da ruwan inabi, wanda yake kai ga lalaci. A maimako haka, ku cika da Ruhu.
Do not get drunk with wine, which is debauchery, but be filled with the Rukha,
19 Ku yi zance da juna cikin zabura, da waƙoƙi, da kuma waƙoƙin ruhaniya. Ku rera, ku kuma yi kiɗe-kiɗe a zuciyarku ga Ubangiji.
speaking to one another in psalms, hymns, and spiritual songs, singing and making music in your heart to the Lord;
20 Kullum ku dinga yin amfani da sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, kuna gode wa Allah Uba a kome.
giving thanks always concerning all things in the name of our Lord Yeshua Meshikha to God the Father;
21 Ku yi biyayya da juna saboda bangirmar da kuke nuna wa Kiristi.
subjecting yourselves one to another in the fear of Meshikha.
22 Matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, kamar ga Ubangiji ne kuke yi.
Wives, submit to your husbands as to the Lord.
23 Gama miji shi ne kan mace, yadda Kiristi yake kai da kuma Mai Ceton ikkilisiya, wadda take jikinsa.
For the husband is the head of the wife, and Meshikha also is the head of the church, being himself the savior of the body.
24 To, kamar yadda ikkilisiya take biyayya ga Kiristi, haka ma ya kamata mata su yi biyayya ga mazansu cikin kome.
But as the church is subject to Meshikha, so let the wives also be to their husbands in everything.
25 Maza, ku ƙaunaci matanku, kamar yadda Kiristi ya ƙaunaci ikkilisiya, ya kuma ba da kansa dominta.
Husbands, love your wives, even as Meshikha also loved the church, and gave himself up for it;
26 Ya mai da ikkilisiya ta zama mai tsarki ta wurin ikon maganarsa, ya kuma tsabtacce ta ta wurin wanke ta da ruwa.
that he might sanctify it, having cleansed it by the washing of water with the word,
27 Kiristi ya yi haka don yă miƙa wa kansa ikkilisiya mai ɗaukaka da kuma mai tsarki, marar aibi, marar tabo, da kuma marar lahani.
that he might present the church to himself gloriously, not having spot or wrinkle or any such thing; but that it should be holy and without blemish.
28 Don haka, dole maza su ƙaunaci matansu kamar yadda suke ƙaunar jikunansu. Wanda yake ƙaunar matarsa, yana ƙaunar kansa ne.
Even so husbands also ought to love their own wives as their own bodies. He who loves his own wife loves himself.
29 Gama ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai yă ciyar da shi, yă kuma kula da shi, kamar yadda Kiristi yake yi wa ikkilisiya,
For no one ever hated his own flesh; but nourishes and cherishes it, even as Meshikha also does the church;
30 gama mu gaɓoɓin jikinsa ne.
because we are members of his body, of his flesh and of his bones.
31 “Saboda haka mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su biyun su zama jiki ɗaya.”
"For this cause a man will leave his father and mother, and will be joined to his wife, and the two will become one flesh."
32 Wannan babban asiri ne, amma na ɗauke shi a matsayin kwatanci ne na Kiristi da ikkilisiya.
This mystery is great, but I speak concerning Meshikha and of the church.
33 Duk da haka, dole kowannenku yă ƙaunaci matarsa kamar yadda yake ƙaunar kansa, kuma dole matar tă yi biyayya ga mijinta.
Nevertheless each of you must also love his own wife even as himself; and let the wife see that she respects her husband.